Uwargidan Gwamnan jihar Gombe, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya,ta jagoranci wani muhimmin taron wayar da kai da nufin ƙarfafa matakan dakilewa da kuma sauya ɗabi’un zamantakewa domin kawo ƙarshen cin zarafin mata da ‘yan mata.
An gudanar da taron ne a Cibiyar Ilimi wato (Education Resource Centre) da ke Tashan Dukku a birnin Gombe, tare da halartar jami’an gwamnati, shugabannin al’umma da na addini, ƙungiyoyin fararen hula, ƙungiyoyin mata, da kuma abokan hulɗar ci gaba.

Shirin, wanda aka aiwatar tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Matan Gwamnonin Nijeriya da kuma tallafin gidauniyar Ford Foundation, ya gudana ne ƙarƙashin taken: “Wayar da Kai don Rigakafi: Sauya Ka’idojin Zamantakewa da Ƙarfafa Ƙudurin Jiha Don Kawar da Cin Zarafin Mata.”
A jawabinta, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya Wacce Kwamishinar Ma’aikatar harkokin Mata Asma’u Mohammed Iganus ta wakilta ta jaddada cewa rigakafi shi ne hanya mafi tasiri wajen magance matsalar cin zarafi sannan ta bayyana cewa sauya tunani da halayen da ke goyon bayan danniya da take hakkin mata na da muhimmanci wajen gina al’umma mai adalci da mutunta juna.

Uwargidan Gwamnan ta kuma tabbatar da ƙudurin gwamnatin Jihar Gombe na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kare haƙƙin mata da ‘yan mata, tare da samar da ingantattun hanyoyin kai ƙorafi da tallafa wa waɗanda abin ya shafa.
Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yi kira ga haɗin kai tsakanin gwamnati, al’umma da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa an kawo ƙarshen cin zarafin mata a kowane mataki. Sun kuma yabawa gwamnatin jihar bisa matakan da take ɗauka wajen ƙarfafa tsarin kariya da inganta walwalar mata da yara.
Taron ya kasance wani muhimmin mataki na ƙara wayar da kai da kuma gina aniyar haɗin gwiwa domin samar da al’umma mai zaman lafiya, adalci da mutunta haƙƙin bil’adama.


