
Yanzu haka dai Yan Najeriya na ci gaba da maida Martani akan dokan zaben Kasar da Majalisar Dattawa ta Amince da ita a ranar talatan nan da tagabata,
Sashen tattara sakamakon zaben ne dai yafi Daukar Hankalin Masu ruwa da tsaki a Harkokin Zaben Najeriyar,
Tsohon mataimakin Shugaban Najeriya Alh.Atiku Abubakar yace abinda Majalisar dattawan tayi a yanzu Akwai rikitarwa..
yace abinda akayi yanzu gaskiya Akwai rudani ace Ayi manuwal ko Kuma na,ura Mai kwakwalwa hakan yama firudar da Mutane akan yadda Lamarin yake abaya na tsari guda na na,ura Mai kwakwalwa.
Atiku Abubakar ya bukaci jam,iyyun Adawa da su hada Kai domin Ganin domin tunkarar Wannan matsala Domin Bai goyi bayan hakan ba,
To Shima Dan Majalisar Wakilan Najeriya Mai wakiltar kananan Hukumomin Rafi,Shiroro,da Muya Hon.Isma,ila Musa Danmodibbo yace Majalisar dattawan ta kwabsa,
Ayanzu dai lokaci ne zai nuna yadda zata kaya a tsakanin majalisar Dattawan da Kuma Yan Kasa Masu ruwa da tsaki akan Lamarin zaben.

