Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fara biyan ‘yan kasar Afghanistan da suka makale a Qatar kudi domin su koma kasar su, a wani yunkur na rufe sansanin da suke zaune, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da shirin sake tsugunar da su a Amurka, domin fargabar da suke yi cewa zaman su a Afghanistan za su fuskanci damuwa da gwamnatin kasar domin alakar su da Amurka, kamar yadda wani babban jami’in ma’aikatar ya gayawa wakilan majalisar dokokin Amurk a ranar laraba.
Fiye da ‘yan kasar Afganistan dubu daya da dari daya ne suke zaune a wani sansanin sojojin Amurka tun farkon shekarar da ta wuce, wadanda masu raji suka ce sun hada da farar hula, da wadanda suka yi ayyuka na musamman da dakarun Amurka, a tsawon shekatu 20 da tayi tana yaki a kasar, wasu daga cikin su iyalan sojojin Amurka ne, wadanda dukkan su za su fuskanci mahadin gaske idan suka koma Afghanistan.
Wakilan majalisar ‘yan democrat sunyi Allah wadai da shirn gwamnatin Trump na biyan ‘yan Afghanistan din, wadanda suk yarda za su koma kasar su, gabannin shirin Amurka na rufe sansanin da suke ciki a cikin watan Maris mai zuwa.
Mataimakin Sakataren harkokin wajen Amurka Paul Kapur yace yayi imani kamar mutum 150 sun karbi kudi kuma sun koma kasar su, sai dai bai san makomar su bayan da suka koma Afghanistan ba.


