Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe ta ce ta samu nasarar ceto wani mutum da aka yi garkuwa da shi a kauyen Tingile, yankin Birin Fulani da ke Karamar Hukumar Nafada a jihar Gombe Najeriya.
A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe uku na daren ranar 11 ga Fabrairu, 2026, lokacin da wasu mutane da ba a san ko su waye ba, dauke da sanduna, adduna da wukake, suka kai hari rumfar kiwon shanun Alhaji Adamu Bappah mai shekaru 48.
Sanarwar ta ce maharan sun doke shi tare da dansa, inda dan ya samu raunuka, kafin daga bisani su yi awon gaba da Alhaji Adamu zuwa wani wuri da ba a sani ba. An garzaya da dansa asibiti domin kula da lafiyarsa.
Sai dai rundunar ta ce cikin gaggawa jami’anta, tare da hadin gwiwar mafarauta da ’yan sa-kai, suka kaddamar da samame a wannan rana da misalin karfe uku na rana. Hakan ya kai ga ceto mutumin a dajin Dawo da ke Karamar Hukumar Kwami.
Bayan ceto shi, an kai shi asibiti domin a duba lafiyarsa kafin daga bisani ya koma hannun iyalansa lafiya.
Rundunar ta kara da cewa ana ci gaba da kokarin cafke wadanda ake zargi da aikata laifin, domin su fuskanci hukunci.
’Yan sandan sun sake jaddada kudurinsu na tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin jihar Gombe.


