Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci
Published: February 13, 2026 at 8:29 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A yau ne ofishin babban kwamishinan sashen kare hakkin dan adam na Majalisar Dinkin Duniya Volker Turk ya ce rundunar ‘yan tawayen Sudan ta RSF sun aikata zalunci matuka da ya karya dokokin yaki lokacin da suka kwato birnin al-Fashir, da kuma yiwuwar aikata laifi na cin zarafin bil-adama.

Birnin na al-Fashir da ke yankin Dafur ya fada hannun ‘yan tawayen ne a watan Octobar bara bayan da dakarun su suka dade suna kewaye da wajen, abin da ya jawo kisan dubbannan mutane.

A hira da aka yi da fiye da mutane 140 da abun ya shafa a arewacin Sudan da kuma gabashin Chad, Ofishin rajin kare hakki na Majalisar Dinkin Duniya ya bada bayanin cewa fiye da mutane 6000 sun rasa rayukan su a kwanaki ukun farko da dakarun RSF suka far ma al-Fashir.

Volker Turk ya kara jaddada kiran sa ga wadanda ke da ruwa da tsaki su dauki matakan da ya kamata don kawo karshen take dokoki da dakarun dake karkashin su suke yi. Ya kuma bukaci kasashe da ke da tasiri su dauki matakin gaggawa don dakile sake afkuwar irin abin da ya faru a al-Fashir.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa
Next Post: Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16 Tsaro
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe
  • Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci
  • Hukumar Zaben Najeriya Ta Sanar Da Ranar Zaben Shugaban Kasa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.