Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana
Published: February 17, 2026 at 9:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin cikin gidan kasar Ghana ya bada labarin cewa ‘yan tawaye masu ikirarin Islama a Burkina Faso sun kashe ‘yan kasar Ghanan su bakwai masu cinikin tumatur, a lokacin da ‘yan bindigar suka kai hari kan wani gari da ake kira Titao dake arewacin Burkina Faso a ranar Asabar data gabata.

Mutanen da harin ya rutsa da su, suna cikin wata tawagar mutum 18 da suka shiga makwabciyar kasar daga arewa, domin su sari tumatur, lokacin da mayakan suka aukawa garin, suka rarrabe maza da mata, daga bisani suka bude musu wuta, kamar yadda ministan ya gayawa wata tashar gidan rediyon kasar.

Minista Mohammed Mubarak Muntaka yace “suka goce da harbe harbe, suka kashe kusan dukkan maza da suke wurin, suka kona gawarwakin su da babbar motar da suke ciki,” har ba’za iya shaida su ba.

Minista Muntaka yace maza uku da mace daya sun tsallake rijiya da baya tare da samun raunuka. Saura mata bakwai dake cikin ayarin sun tsere ba tare da sun jikkata ba.

Daga bisani ya dauki hukumomi a Burkina Faso sa’o’i masu yawa suka sake kwato iko kan garin, kamar yadda ministan ya fada, ya kara da cewa, jami’an na Burkina Fason, sunyi alkawarin bada kariyan soja ga sauran tawagar da wadanda suka jikkata zuwa ofishin jakadancin Ghana dake birnin Ouagadougou, babban birnin kasar ta Burkina Faso.

Afrika, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya
Next Post: Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai
Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
Nuhu Ribadu Ya Mika Yara 130 Da Aka Kubutar Ga Gwamna Bago Tsaro
Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye
  • Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa
  • Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Hatsarin Mota Yayi Ajalin Mutum 7 A Gombe Najeriya
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.