Shugaba Tinubu ya sanya hannu kan sabuwar dokar zaɓe
Shugaban Kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanya hannu kan sabuwar dokar zabe ta shekarar 2022, da aka yi wa garambawul zuwa ta shekarar 2026.

Hakan ya biyo bayan amincewar Majalisar Dokoki ta Ƙasa da kudurin dokar a ranar Talata, bayan shafe watanni ana muhawara da tattaunawa a kansa.


