Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka
Published: February 25, 2026 at 9:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Fafaroma Leo zai ziyarci kasashe hudu a fadin Afirka daga ranar 13 zuwa 23 ga Afrilu, fadar Vatican ta sanar a ranar Laraba, inda Fafaroma ya yi ziyararsa ta farko zuwa ketare a shekarar 2026 zuwa nahiyar da cocin Katolika ke ci gaba da bunkasa.

Fafaroma zai kuma kai ziyarar kwana guda a ranar 28 ga Maris a birnin Monaco, karamar hukumar da ke gabar tekun Faransa, kuma zai ziyarci Spain daga ranakun 6-12 ga watan Yuni, in ji fadar Vatican.

Kasashen da zai ziyar ta A Afirka, sun hada da Algeria, Angola, Equatorial Guinea da Kamaru. Ana sa ran zai jawo dimbin jama’a, ya bukaci shugabannin kasashen duniya da su goyi bayan ci gaba a nahiyar, da kuma bayyana kokarin da ake yi a tattaunawar Katolika da Musulmi.

Leo, wanda aka zaba a watan Mayu domin ya gaji marigayi Fafaroma Francis a matsayin shugaban cocin mai mutane biliyan 1.4, ya yi balaguro daya kacal zuwa ketare ya zuwa yanzu, inda ya ziyarci Turkiyya da Lebanon a watan Nuwamba da Disamba a ziyarar da aka shirya wa Francis.

Amurka, Labarai, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka
Next Post: An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
Shugaban Kasar Ghana Ya Soki Manufofin Gwamnatin Amurka Afrika
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
  • Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.