Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki
Published: February 26, 2026 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Afrika ta kudu da Kenya a ranar Alhamis suke kara bayyana cewa ‘yan kasashen masu yawa ne aka yaudare su shiga yakin Rasha da Ukraine, domin hukumomi a Pretoria sun bada rahoton ‘yan kasar biyu sun mutu a fagen daga, yayinda wata kotu a Nairobi ta tuhumi wani mutum da laifin safarar ‘yan kasar 25 domin suyi yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Afrika ta kudu ta fada cewa ‘yan kasar biyu da suka mutu a fagen yaki basa cikin ‘yan kasar su 17 da aka yaudara suka taya Rasha yaki a Ukraine, wadanda galibin su an ceto su sun koma kasar, kamar yadda wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Alhamis. Ma’aikatar bata fadi lokaci da kuma yanayin da ya kai ga mutuwar mutanen biyu ba.

Hukumomin Rasha sun musanta cewa suna daukar ‘yan kasashen Afirka aikin soja ba bisa ka’ida ba domin yakinta da Ukraine.

“gwamnati tana ci gaba da binciken kungiyoyi da suke da hanu wajen daukar ‘yan kasa zuwa Rasha, da zummar hukunta dukkan wadanda suke da hanu ciki,” kamar yadda doka ta tanada, ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta kudun ta fada.

A Nairobi, kotu ta tuhumi wani dan kasar mai suna Festus Arasa Omwamba, darektan wani kamfanin samarwa mutane ayyyukan yi da laifin safarar mutane zuwa Rasha ta hanyoyin yaudara, kamar yadda ofishin Daraktan gabatar da kararraki na kasar ya fada.

Ma’aikatar shari’ar tace an ceto mutane 22 cikin 25, a wani daki a karamar hukumar Machakos da bashi da nisa da babban birnin kasar cikin watan Nuwamban bara. Uku daga cikin wannan adadi tuni suka sapmi kansu a fagen daga a Ukraine.

Fiye da ‘yan kasashen Afirka dubu daya da dari bakwai ne suke yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi
Next Post: Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato Afrika
Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
Kasar Namibiya Tayi Watsi Da Yarjejeniya Tsakanin Ta Da Kamfanin Total Labarai
IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli Afrika
  • Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA Afrika
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Baba Malam Ya Lallasa Abokan Hamayya Da Kuri’u Sama Da Dubu 236 A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.