Hukumomin Taliban sun ce a shirye suke da suyi tattaunawar sulhu, bayan da Pakistan ta kaiwa rundunar sojin su harin bomb a manyan birane, inda ta hallaka gomman su.
Wannan shine karon farko da Pakistan ta kai hari kai tsaye ga ‘yan kawancen nata a da, inda ta yi zargin suna bawa ‘yan ta’adda mafaka. Ta ce wannan yaki ne kai tsaye.
Pakistan ta kai hari Kabul, babban birnin Afghanistan da birnin Kandahar, inda nan ne shugabannin Taliban suke, wannan na nuna tabarbarewar alaka tsakanin makwabtan biyu.
Hukumomin tsaro a Pakistan sun ce an kaiwa ofisoshi da sansanin sojojin Taliban harin ne ta sama da ta kasa don mai da martani kan harin da sojin Afghanistan suka kai ranar Alhamis.


