Shugaban Amurka Donald Trump, ya fada Alhamis din nan cewa, yana da hakkin tsoma baki kan wadda Iran zata zaba a zaman shugaban kasarta, yayinda yakin yake kara tsanani, inda jiragen yakin Amurkan dana Isra’il suke ci gaba da kai hare hare a fadin kasar Farisan, su kuma kasashe dake yankin Gilf suke fuskantar sabbin hare hare daga Iran.
A hira da yayi da kamfanin dillancin labarai na Reuters, Trump yace ko kusa Mojtaba Khameni, dan tsohon shugaban addinin kasar, marigayi Ayatollah Ali Khameni, mai ra’ayin mazan jiya, ba shine mutuminda ya dace ya gaji mahaifinsa ba.
“Muna so mu kasance cikin shawarar zaben mutuminda zai jagoranci Iran,” Mr. Trump ya fada ta woyar tarho.
Kalaman na Mr. Trump suna zuwa ne a dai dai lokacin da sojojin Isra’ila suka gargadi mazauna kasar ciki harda wadadanda suke gabashin birnin Tehran da su tashi, yayinda wata kafar yada labarai na Iran ya bada labarin jin karar fashe fashe a sassan birnin daban daban.


