Shugaban Amurka Donald Trump, ya fada ranar Alhamis cewa, hukumomi a Tehran suna kiran Washington da nufin su kulla yarjejeniya, a dai dai lokacin da jiragen yakin Amurka da Isra’ila suke ci gaba da luguden wuta kan kasar, ya kara da cewa tilas ne a dauki matakai da za su sassauta matsalar jigilar mai.
Yana mai cewa, “suna kira da cewa yaya za’ayi mu kulla yarjejeniya, nace ai kusan kun makara,” inji Trump yayin wani biki a fadar WH lokacin da Kungiyar kwallon kafa daga jahar Miami da ake kira Inter Milan ta kai masa ziyara.
Trump yayi magana kan nasarori da dakarun Amurka suke samu a yakin, yana cewa suna rusa karfin Iran na amfani da makamai masu linzami da kuma jiragen yaki maras matuka da ake kira drones da turanci. Ya kara da cewa jiragen yakin ruwan Farisa sun tarwatse yace Amurka ta lalata ko ta nutsar da jiragen ruwa na yaki na Iran 24 cikin kwanaki uku. Daga nan yayi kira ga jakadun Iran a fadin duniya su nemi mafaka, domin su taimaka wajen ginawa Farisa makoma mai kyau
Shugaban Amurka Donald Trump, ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa ko kusa Mujtaba Ali Khameni, wanda shine akan gaba a goyon bayan wadanda mahukunta a Farisa suke duba yi yuwar a nada su a zaman sabon shugaban addinin Iran. Trump yace wajibi ne ya tsoma baki kan wadda Iran zata zaba a zaman shugaban kasarta, shigen abunda yayi a Venezuela.


