‘Yan sanda a Najeriya sun yi nasarar hallaka ‘yan ta’adda 45 a kauyen Dan Musa dake jihar Katsina, a cewar wani jawabi daga gwamnatin jihar ranar Asabar.
Tashin hankalin ya biyo bayan wani Hari da ‘yan bindiga daga jihar Zamfara suka kai kauyen Alhazawa dake garin Musawa ranar 5 ga wannan Watan, suka yi kokarin sace shanu.
Maharan sun sake dawowa washegari, inda anan suka yi arangama da jami’an tsaro da aka girke a sansanin soji na Dan Ali kusa da unguwar Maidabawa. A nan ne Jami’an tsaron suka yi nasarar hallaka mutane 45 daga cikin su. Wani kaftin da sojoji biyu suma sun rasa ran su a fadan.


