Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba
Published: March 10, 2026 at 4:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani rahoton bayanan leken asiri na Amurka da aka rubuta shi jim kadan kafin Amurka da Isra’ila su far ma kasar Iran da hare-hare, ya cimma daidaito a kan cewa hare-haren sojan Amurka ba zasu iya kawo sauyin shugabanci a kasar ba.

Wasu majiyoyi biyu da suka ga wannan rahoton da hukumomin leken asirin Amurka karkashin inuwar Majalisar Ayyukan Leken Asiri ta kasa suka rubuta a cikin watan Fabrairu, sun ce rahoton ya tsayar da shawarar cewa kai hare-hare ta sama ko kuma jimawa ana kai wadannan hare-haren, zai yi wuya su haifar da sabuwar gwamnati a Iran.

Majiyoyin suka ce rahoton ya ce koda an kashe dukkan shugabannin kasar na yanzu, zai yi wuya a iya canja gwamnatin kasar.

Wannan bayanin, ya gurgunta ikirarin da gwamnatin shugaba Trump take yi cewa zata iya cimma burinta na kai farmakin kan Iran cikin kankanin lokaci.

Mutanen biyu, wadanda suka bukaci da a sakaye sunayensu sun fada ma kamfanin dillancin labaran Associated Press cewa hukumomin leken asirin na Amurka sun cimma daidaito kan cewa babu wasu ‘yan adawa dake da karfi ko hadin kan da zasu iya karbar mulki a kasar Iran ko da an kashe shugabannin kasar.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa
Next Post: Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata

Karin Labarai Masu Alaka

EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
Kasar Amurka Tabada Tabbacin Bawa Ukraine Tsaron Shekarun 15 Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.