Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 11, 2026 at 4:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Da yai magana kan rikicin na gabas ta tsakiya, shugaban majalisar tarayyar turai, Antonio Costa, ya fada ranar talata cewa Rasha ce take cin ribar yakin da ake yi a gabas ta tsakiya, ganin farashin mai ya tashi, kuma ya kauda hankali daga yakin da take da Ukraine.

“Zuwa yanzu dai kasa daya ce ta sami nasarar wannan yaki,” itace Rasha, Costa ya fada a wani jawabi da yayi wa jakadun Kungiyar tarayyar turai.

Antonio Costa, ya jaddada bukatar kungiyar tarayyar turai ta kare tsarin duniya na bin doka da oda, wadda yace ahalin yanzu Amurka take yi wa kalubale, daga nan ya shawarwaci duka sassa a rikicin na gabas ta tsakiyya, su koma teburin shawarwari.

Ahalinda ake ciki kuma, farashin mai ya fadi da kamar kashi 15 cikin dari ranar talata, kwana daya bayanda mai yayi tashin goron zabbi, rabon da ya kai haka tun 2022, faduwar farashin ya biyo bayan kalaman shugaban Amurka Trump cewa yakin ya kusa zuwa karshe.

Yau mai da ake kira Brent ana cinikinsa kan dala 84 da centi 73 kan ko wani gangar danyen mai, yayinda wadda ake kira West Texas shi kuma ya tashi kan dala 80 da centi 31. Farashin ya kara faduwa, bayan da ministan makamashi na Amurka Chris Wright ya rubuta a shafinsa na X cewa, sojojin Amurka sun taimaka an wuce da mai ta mashigan ruwa na Hormuz.

Wannan lamari na tsadar mai yana kalubale ga rinjayen da jam’iyyar Republican take dashi a zaben rabin wa’adi mai zuwa, kamar dai yadda masu nazarin harkokin yau da kullum suke hasashe.

Har yanzu dai kan yakin na gabas ta tsakiya, Australia zata tura jirgin leken asiri zuwa gabas ta tsakiya, kuma zata aike da makamai masu linzami zuwa hadaddiyar daular larabawa, amma ba zata tura sojojinta na kasa zuwa Iran ba, PM kasar Anthony Albanese ya fada a ranar talata.

Albanese yace, taimakon da Australia take da kayan yaki, zai taimakawa kasashe da suke yankin Gulf su kare kan su daga hare hare daga Iran ba babu hujja.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Next Post: Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Akwai Doka Mai Tsanani Wajen Mallakar Bindiga A Kasashen Yammacin Turai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.