Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya
Published: March 11, 2026 at 4:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Da yai magana kan rikicin na gabas ta tsakiya, shugaban majalisar tarayyar turai, Antonio Costa, ya fada ranar talata cewa Rasha ce take cin ribar yakin da ake yi a gabas ta tsakiya, ganin farashin mai ya tashi, kuma ya kauda hankali daga yakin da take da Ukraine.

“Zuwa yanzu dai kasa daya ce ta sami nasarar wannan yaki,” itace Rasha, Costa ya fada a wani jawabi da yayi wa jakadun Kungiyar tarayyar turai.

Antonio Costa, ya jaddada bukatar kungiyar tarayyar turai ta kare tsarin duniya na bin doka da oda, wadda yace ahalin yanzu Amurka take yi wa kalubale, daga nan ya shawarwaci duka sassa a rikicin na gabas ta tsakiyya, su koma teburin shawarwari.

Ahalinda ake ciki kuma, farashin mai ya fadi da kamar kashi 15 cikin dari ranar talata, kwana daya bayanda mai yayi tashin goron zabbi, rabon da ya kai haka tun 2022, faduwar farashin ya biyo bayan kalaman shugaban Amurka Trump cewa yakin ya kusa zuwa karshe.

Yau mai da ake kira Brent ana cinikinsa kan dala 84 da centi 73 kan ko wani gangar danyen mai, yayinda wadda ake kira West Texas shi kuma ya tashi kan dala 80 da centi 31. Farashin ya kara faduwa, bayan da ministan makamashi na Amurka Chris Wright ya rubuta a shafinsa na X cewa, sojojin Amurka sun taimaka an wuce da mai ta mashigan ruwa na Hormuz.

Wannan lamari na tsadar mai yana kalubale ga rinjayen da jam’iyyar Republican take dashi a zaben rabin wa’adi mai zuwa, kamar dai yadda masu nazarin harkokin yau da kullum suke hasashe.

Har yanzu dai kan yakin na gabas ta tsakiya, Australia zata tura jirgin leken asiri zuwa gabas ta tsakiya, kuma zata aike da makamai masu linzami zuwa hadaddiyar daular larabawa, amma ba zata tura sojojinta na kasa zuwa Iran ba, PM kasar Anthony Albanese ya fada a ranar talata.

Albanese yace, taimakon da Australia take da kayan yaki, zai taimakawa kasashe da suke yankin Gulf su kare kan su daga hare hare daga Iran ba babu hujja.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran
Next Post: Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
Majalisa A Kasar Somaliya Ta Amince Da Sauya Tsarin Mulkin Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rikicin Hakar Gwal Ya Janyo Hallaka Mutane 70 A Sudan Ta Kudu Afrika
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Domin Inganta Tsaro Najeriya Ta Sayi Jiragen Yaki A Kasar Italiya Tsaro
  • Thailand Da Cambodia Sun Fara Tattauunawa Kan Batun Tsagaita Wuta Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.