Eswatini ta ce ta samu karin mutane hudu da aka kora daga kasar Amurka ranar Alhamis, wanda ya kai adadin zuwa akalla mutum 19 yayin da gwamnatin Trump ke ci gaba da yaki da bakin haure.
Biyu daga cikin sabbin ‘yan gudun hijirar sun fito ne daga Somalia, daya daga Sudan, daya kuma daga Tanzaniya. Wadanda aka kora a baya, wadanda suka isa a watan Yulin bara, sun hada da ‘yan kasashen Vietnam, Cuba, Laos da Yemen.
Lauyan wasu daga cikin waccan kungiyar ta farko, Alma David, ya shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa wani dan kasar Cambodia, Pheap Rom, ya kamata a dawo da shi gida, na biyu da za a sake shi bayan an mayar da wani mutum Jamaica a bara.
Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump ta biya karamar kasar da ke kudancin Afirka dala miliyan 5.1 domin karbarsu.
“A bisa ga wannan yarjejeniyar al’ummar kasar sun sake karbar wani rukunin ‘yan kasashe hudu daga Amurka,” in ji sanarwar da gwamnatin Eswatini, wata cikakkiyar masarautu da Sarki Mswati III ke mulki.


