Mutane 62 ne, ciki har da yara 8, suka rasa rayukan su sakamakon ruwan sama mai karfi da ya haddasa ambaliyar ruwa a Nairobi, babban birnin kasar Kenya, da kuma wasu yankunan a karshen makon jiya, a cewar ‘yan sanda a ranar Asabar.
Mafi munin abun ya afku a babban birnin na Nairobi inda mutane 33 suka rasu a cewar ‘yan sanda bayyana adadin mutanen da suka rasa rayukan su a shafin sada zumunta na X.
Fiye da magidanta 2000, sun rasa matsuguni, yayin da ake ci gaba da tafka ruwan sama a yankuna da dama.
Ma’aikatan bada agaji sun fara zakulo gawarwakin mutane daga ruwa a sassa daban daban na birnin Nairobi tun Asabar din da ta gabata, bayan da ambaliyar ruwa cikin dare ya tafi da motoci da dama, ya kuma kawo tsaiko ga zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin sama mafi girma a gabashin Afirka.


