Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
Published: March 17, 2026 at 10:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya, karkashin jagorancin Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta yi Ala-wadai da harin bama-bamai da ya auku a birnin Maiduguri na jihar Borno, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da jikkatar mutane da dama.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ta bakin shugaban kungiyar, Inuwa Yahaya, gwamnonin sun bayyana harin a matsayin abin takaici da kuma babbar barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma a yankin Arewa maso Gabas. Sun jajantawa gwamnatin jihar Borno da iyalan wadanda abin ya shafa, tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama, ya kuma bai wa wadanda suka jikkata lafiya.

Kungiyar ta bukaci hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen bincike domin gano wadanda ke da hannu a harin, tare da tabbatar da an hukunta su bisa doka.

Haka zalika, sun jaddada bukatar daukar matakan gaggawa domin kawo karshen irin wadannan hare-hare, tare da karfafa tsaro musamman a wuraren taruwar jama’a.

Gwamnonin sun kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara tallafawa rundunonin tsaro da kayan aiki na zamani, da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da al’umma domin dakile ayyukan ta’addanci a fadin yankin.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
Kuɗaɗen Da EFCC Ta Kwato Za Su Tallafa Wa Shirin Lamunin Karatu Afrika
Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
  • NANPAN Ta Wayar Da Al’umma Kan Amfanin Shayar Da Jarirai Nono Kaɗai Afrika
  • Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi Labarai
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.