Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya kira harin da aka kai a Maiduguri babban birnin jahar Barno birni da yake da matukar tsaro, wanda ya janyo mutuwar mutane 23, a zaman take-taken dan kada da ruwa yake karewa ga ‘yan bindiga, wadanda suke son yada tsoro. Sai da masana suna cewa harin sabanin yadda shugaba Tinubu yake kallon lamarin ne, saboda aganin su wannan alama ce ta karfin da mayakan sakan suke dashi
Kwararrun wadanda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa ra’ayoyin su sunce harin da aka kai a Maiduguri alama ce gazawar hukumomi na samun bayanan sirri, da kuma karfin da mayakan sakai masu ikirarin bin tafarkin musulunci suke dashi na afkawa birane duk kuwa da matakan da gwamnati take dauka akan su.
Har yanzu babu tabbas kan ko wace kungiya ce cikin kungiyoyin ‘yan bindiga a kasar suka kai harin, wadda yake gwada sarkakiyar fitinar da ‘yan tawayen suke yi na tsawon shekaru 17, wadda ya halaka dubun dubatan mutane, da kuma tilasta miliyyin mutane barin muhallan su.


