Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma
Published: March 19, 2026 at 2:11 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 19, 2026

Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara Ta kasa Reshen Jihar Gombe, Ta Fidda Jawabai Domin Kare Lafiyar Al’umma.

Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya reshen jihar Gombe, DCF Suleiman Mohammed Suleiman, ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan, tare da kira ga mazauna jihar da su gudanar da bukukuwan Sallah cikin kulawa da tsaro.

Kwarewa ta nuna cewa a lokutan bukukuwa ana yawan samun aukuwar gobara da wasu hatsarori da za a iya kaucewa, sakamakon karuwar ayyuka a gida da kasuwanci. Saboda haka, Hukumar na kira ga jama’a da su dauki matakan kariya a kowane lokaci.

Ana shawartar mazauna da su kula da yadda suke sarrafa silinda na gas da kayan lantarki, su guji barin girki ba tare da kulawa ba, sannan su nisanci lodin wutar lantarki fiye da kima. Haka kuma, dole ne a rika amfani da janareto a waje mai isasshen iska, yayin da ake bukatar a adana abubuwa masu kamawa da wuta a wurare masu aminci, nesa da zafi.

A lokacin taruka, ana bukatar kulawa da yara, samar da isasshen iska, da kuma kiyaye doka da oda. Haka kuma, a guji yin ajiye motoci ba bisa ka’ida ba wanda zai iya hana motocin agaji wucewa.

Dangane da yanayin zafi da ake ciki a halin yanzu, ana kara jaddada wa jama’a da su rika shan ruwa sosai, su rage kasancewa cikin tsananin zafi, tare da lura da alamomin cututtukan da ke da nasaba da zafi.

Hukumar ta kuma ja hankalin jama’a kan hadarin da ke tattare da rashin kula wajen sarrafawa da adana man fetur. Don haka ana kira ga kowa da kowa da ya yi taka-tsantsan musamman a gidaje da kuma wuraren sayar da mai.

Idan wata gobara ko wani hatsari ya faru, yana da matukar muhimmanci a kai rahoto cikin gaggawa ta wadannan lambobi: Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, Reshen Jihar Gombe: 070-314-97455

Lambar Gaggawa ta Kasa: 112

Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya reshen Jihar Gombe na nan a shirye domin daukar mataki a kowane lokaci, tare da jaddada cewa kare lafiyar jama’a alhaki ne na kowa da kowa.

Afrika, Kimiya, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey
Next Post: Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Kasar Masar Ta Dakatar Da Wasu Ayyukan Da Ake Amfani Da Man Fetur Da Diesel Labarai
China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
Trump Da Bin Salman Da Wasu Kasashe Za Su Sa Hannu A Rikicin Sudan Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Yakin Rasha Da Ukrain Babban Kalubale Ne Ga Kasashen Turai Labarai
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.