Iran ta sanarwa masu shiga tsakani cewa, dole ne a haɗa da ƙasar Lebanon a cikin duk wata yarjejeniyar tsagaita wuta da za a cimma da Amurka da Isra’ila, kamar yadda wasu majiyoyi shida daga yankin da suka san matsayin Iran suka bayyana. Hakan na nuni da cewa, kawo ƙarshen yaƙin yana da alaƙa da dakatar da hare-haren Isra’ila kan ƙungiyar Hezbollah.
Tashar Press TV ta Iran ta rawaito a jiya Laraba cewa wani jami’in Iran ya ce Tehran na son duk wata yarjejeniya da Amurka ta tabbatar da kawo ƙarshen yaƙin, ba kawai a kanta ba har ma da sauran ƙungiyoyin “gwagwarmaya” a yankin.
Wani babban jami’in Iran ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters duk a jiya Laraba cewa, har yanzu Tehran na nazarin shawarar Amurka na kawo ƙarshen rikicin yankin, da ya kwashe kusan wata guda yana gudana, abin da ke nuna cewa Iran ba ta yi watsi da shawarar gaba ɗaya ba har yanzu.
Majiyoyi shida daga yankin, waɗanda suka nemi a sakaya sunayensu saboda muhimmancin batun, sun ce Tehran ta sanar da masu shiga tsakani tun daga tsakiyar watan Maris cewa, tana neman yarjejeniya da za ta kuma dakatar da hare-haren Isra’ila kan ƙungiyar Hezbollah ta Lebanon.


