Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon
Published: March 30, 2026 at 9:20 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana a ranar Lahadi cewar, ya umarci rundunar sojoji da ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a kudancin Lebanon, yana mai danganta hakan da ci gaba da harba rokokin da ƙungiyar Hezbollah ke yi.

Isra’ila ta ce a makon da ya gabata tana ƙara faɗaɗa wani “yakin kariya” har zuwa kogin Litani. Sai dai ba a bayyana kai tsaye ko Netanyahu na nufin wannan yanki ba ne ko kuma a yankin da suka ƙwace yanzu.

Netanyahu ya ce a cikin wani bidiyo da ya fitar daga hedikwatar rundunar arewacin Isra’ila cewa: “Na bayar da umarni a ƙara faɗaɗa yankin tsaro da ake da shi domin a ƙarshe a kawar da barazanar kutse, tare da tura hare-haren makaman roka masu lalata tankuna daga kan iyakokinmu.”

Ofishinsa ya ƙi bayar da ƙarin bayani, sannan har yanzu ba a tattauna wannan batu a majalisar tsaron ƙasar ba.

A makon da ya gabata, Ministan Tsaro Israel Katz ya ce sojojin Isra’ila za su “ci gaba da riƙe sauran gadoji da yankin tsaro har zuwa kogin Litani,” wanda ke haɗuwa da Tekun Bahar Rum kusan kilomita 30 arewa da iyakar Isra’ila.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund
Next Post: Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
  • Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Majalisun Najeriya Sun Amince Ta Karin Kasafin Kudi Afrika
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.