Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana a ranar Lahadi cewar, ya umarci rundunar sojoji da ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a kudancin Lebanon, yana mai danganta hakan da ci gaba da harba rokokin da ƙungiyar Hezbollah ke yi.
Isra’ila ta ce a makon da ya gabata tana ƙara faɗaɗa wani “yakin kariya” har zuwa kogin Litani. Sai dai ba a bayyana kai tsaye ko Netanyahu na nufin wannan yanki ba ne ko kuma a yankin da suka ƙwace yanzu.
Netanyahu ya ce a cikin wani bidiyo da ya fitar daga hedikwatar rundunar arewacin Isra’ila cewa: “Na bayar da umarni a ƙara faɗaɗa yankin tsaro da ake da shi domin a ƙarshe a kawar da barazanar kutse, tare da tura hare-haren makaman roka masu lalata tankuna daga kan iyakokinmu.”
Ofishinsa ya ƙi bayar da ƙarin bayani, sannan har yanzu ba a tattauna wannan batu a majalisar tsaron ƙasar ba.
A makon da ya gabata, Ministan Tsaro Israel Katz ya ce sojojin Isra’ila za su “ci gaba da riƙe sauran gadoji da yankin tsaro har zuwa kogin Litani,” wanda ke haɗuwa da Tekun Bahar Rum kusan kilomita 30 arewa da iyakar Isra’ila.


