Kungiyar Direbobin dakon Mai ta Najeriya Wato NUPENG ta rantsar da Sabon Shugabanta na Yankin Arewacin Najeriya a hedkwatar Kungiyar dake kaduna a dai dai lokacin da Direbobin Ke fama da Matsalar Rashin kyawun hanya a Kasar.

Tun a baya dai Direbobin dakon man sun sha bayyana damuwarsu tare da nunawa Hukumomin Najeriyar matukar bukatarsu na ganin an gyara Hanyoyin mota da Suka hada Arewacin Najeriya da Kuma kudancin Kasar,
Kwamred Faruk kawo shine Sabon shugaban kungiyar Direbobin ta NUPENG na jihohin Arewacin Najeriya 19 yace a yanzu zai maida hankali wajan Matsawa Gwamnatin Najeriya lamba Domin ta wai wayi Hanyoyin Kasar da akasarinsu sun fita hayyacinsu kamar yadda yayi Mani Karin bayani Jim kadan bayan kammala Shan rantsuwar.

Bayanai dai sun cewa Direbobi Dama Suka su Masu motcin suna tabka Asarar da milyoyin Kudi dama rasa rayukkan Mutane duk safiya ta akan Manyan Hanyoyin Nigeria kamar yadda Kwamred Faruk kawo yayi Karin bayani.
A yanzu Yan Najeriya Musamman ta Arewa na cike da fatar ganin Sabon Shugaban Kungiyar ta NUPENG ya Samu Nasarar Shawo. Kan Gwamnatin Najeriyar domin ta waiwayi Hanyoyin cikin hanzari ta yadda Yan Kasa zasu Samu sa,ida.
Daga Minna Ga Rahoton Wakilin Amurka Ke Magana Mustapha Nasiru Batsari


