Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote
Published: April 1, 2026 at 3:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 1, 2026

Gwamnatin tarayyar Najeriya da ta jihar Kano da kuma gidauniyar rukunin kamfanonin Dangote, sun cimma yarjejeniyar haɓakawa, tare da kula da babbar cibiyar koyon sana’o’i ta Dangote (Dangote Ultramodern Skills Acquisition Center) da ke birnin Kano.

Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar Ilimin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (STSB), Farfesa Dahiru Sale Mohammed, ya fitar a madadin Kwamishinan Ilimi na jihar.

A karkashin wannan sabuwar dangantaka, ɓangarorin uku za su dauki nauyin garambawul da inganta kayan aikin cibiyar, sannan su tabbatar da dorewar ayyukanta na tsawon shekaru 20 masu zuwa.

Cibiyar, wacce aka gina domin bai wa matasa horo kan kwarewar hannu da fasahar zamani, ana sa ran za ta kasance kashin baya wajen rage radadin rashin aikin yi a jihar ta Kano da ma makwabtanta.

Farfesa Dahiru Sale ya bayyana cewa wannan yunkuri zai tabbatar da cewa cibiyar ba ta durkushe ba kamar yadda wasu ayyukan ke yi idan aka samu canjin gwamnati, duba da tsarin kula da ita na dogon lokaci da aka kulla.

Jihar Kano dai ita ce jiha mafi yawan jama’a a arewacin Najeriya, inda matasa ke da kaso mafi tsoka. Wannan cibiya za ta mayar da hankali ne wajen koyar da sana’o’in da suka dace da bukatun karni na 21, domin ba wa matasa damar dogaro da kansu maimakon jiran aikin gwamnati.

Sanarwar ta jaddada cewa an kammala dukkan shirye-shiryen fara aikin fito da sabuwar fuskar cibiyar nan ba da jimawa ba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya
Next Post: Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yagana Da Shugaban Sa’ido Akan Nukiliya Afrika
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
  • NFF, Ta Umarci Tawagar Masu Horas Da Super Falcons Su Sauka Daga Bakin Aiki Nan Take Wasanni
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.