Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai gabatar da kuri’a ranar Jumu’a kan kudurin da kasar Bahrain ta gabatar na kariya ga jigilar kayayyakin kasuwanci a ciki da kewayen mashigin ruwa na Hormuz, a cewar jakadu, amma China dake da damar ikon hanawa, ta nuna karara rashin goyon bayan ta ga bada damar amfani da karfi.
Farashin mai ya tashi tun bayan da Amurka da Isra’ila suka farwa Iran a karshen watan Fabrairu, abinda ya janyo yaki da yaki ci yaki cinyewa fiye da wata daya, ya kuma jawo hana jiragen dakon mai wucewa ta mashigin ruwa na Hormuz.
Jakadun kasashe sunce kasar Bahrain, wacce itace a yanzu take rike da shugabancin kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ta gama tsara daftarin kuduri, wanda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya samu gani, da zai bada dama Ayi amfani da duk wani mataki na tsaro da ya wajabta don wanzar da kariya ga sufurin kayayyakin kasuwanci.


