Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare
Published: April 10, 2026 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A Najeriya gamayyar mayakan kungiyar Boko Harama da ISWAP sun kai hari na hadin baki cikin dare kan sansanoni daban daban a jihar Barno, har suka kashe wani janar da wasu sojojin kasar, kamar yadda wasu majiyoyin soji suka fada ranar Ahamis.

Helkwatar mayakan kasar, sunce mayakan sun kai hari kan wata cibiyar sojoji da ke Benisheikh amma aka taka musu birki, ta tabbatar da an kashe sojoji a artabun, helkawatar ta bukaci jama’a su dakaci karin bayani dangane da wadanda rikicin ya shafa.

Mayakan sun fara kai hari ne kan garuruwan Pulka, da Bakin ruwa wadanda suke karamar hukumar Gwoza a daren laraba, sannan suka yi kokarin kama helkwatar runduna ta musamman ta 29 dake Benisheikh da tsakar dare, inji helkwatar ta mayakan Najeriya. Ta kara da cewa sojojin Najeriya suka ja daga karkashin jagorancin janar Oseni Braimah suka fatattaki ‘yan bindigar.

Sai dai wasu majiyoyin soja biyu sun fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ‘yan bindigar sunyi dai dai da sansanin da yake Benisheikh, suka kashe janar Oseni Braimah, da wasu sojoji cikin su har da wani mai mukamin keftin, suka lalata motocin soja masu yawa. Kamfanin dillancin labarai na Reuters bashi da tabbaciin wannan labari.

Wani jami’in soja, wanda yana daga cikin wadanda suka kai dauki a Benisheikh, yace jiragen yaki ta sama su suka yi jigilar wadanda suka kwanta dama a harin na Benisheikh a ranar Alhamis, bayanda suka taimaka wajen korar ‘yan binidgar wadanda suka yi sa’o’I uku suna barna a yankin.

Ahalinda ake ciki kuma, rassan kungiyoyin al-qeada da ISIS a yammacin Afirka a karon farko sun baiwa hamata iska a Nijar, kamar yadda wata sanarwa da daya daga cikin kungiyoyin ta bayar, mataki a masu fashin baki suka ce ya karfafa gababar da take tsakanin kungiyoyin na shekara da shekaru.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa
Next Post: Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe Labarai
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai
CHAN Ta Duba Lafiyar Idanun ‘Yan Jarida A Filato Afrika
Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
  • Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.