A Najeriya gamayyar mayakan kungiyar Boko Harama da ISWAP sun kai hari na hadin baki cikin dare kan sansanoni daban daban a jihar Barno, har suka kashe wani janar da wasu sojojin kasar, kamar yadda wasu majiyoyin soji suka fada ranar Ahamis.
Helkwatar mayakan kasar, sunce mayakan sun kai hari kan wata cibiyar sojoji da ke Benisheikh amma aka taka musu birki, ta tabbatar da an kashe sojoji a artabun, helkawatar ta bukaci jama’a su dakaci karin bayani dangane da wadanda rikicin ya shafa.
Mayakan sun fara kai hari ne kan garuruwan Pulka, da Bakin ruwa wadanda suke karamar hukumar Gwoza a daren laraba, sannan suka yi kokarin kama helkwatar runduna ta musamman ta 29 dake Benisheikh da tsakar dare, inji helkwatar ta mayakan Najeriya. Ta kara da cewa sojojin Najeriya suka ja daga karkashin jagorancin janar Oseni Braimah suka fatattaki ‘yan bindigar.
Sai dai wasu majiyoyin soja biyu sun fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ‘yan bindigar sunyi dai dai da sansanin da yake Benisheikh, suka kashe janar Oseni Braimah, da wasu sojoji cikin su har da wani mai mukamin keftin, suka lalata motocin soja masu yawa. Kamfanin dillancin labarai na Reuters bashi da tabbaciin wannan labari.
Wani jami’in soja, wanda yana daga cikin wadanda suka kai dauki a Benisheikh, yace jiragen yaki ta sama su suka yi jigilar wadanda suka kwanta dama a harin na Benisheikh a ranar Alhamis, bayanda suka taimaka wajen korar ‘yan binidgar wadanda suka yi sa’o’I uku suna barna a yankin.
Ahalinda ake ciki kuma, rassan kungiyoyin al-qeada da ISIS a yammacin Afirka a karon farko sun baiwa hamata iska a Nijar, kamar yadda wata sanarwa da daya daga cikin kungiyoyin ta bayar, mataki a masu fashin baki suka ce ya karfafa gababar da take tsakanin kungiyoyin na shekara da shekaru.


