Jami’an Rundunar Karewa Al’umma a jihar Zamfara, da aka fi sani da “Askarawa”, sun kama wasu na’urorin fashewa, makudan kuɗaɗe, da sauran kayan tallafi da ake zargin za’a kaiwa ’yan bindiga a ƙauyen Bindin da ke Ƙaramar Hukumar Maru.
Kwamandan rundunar CPG na jihar, AIG Shehu Muhammad Dalijan (mai ritaya), ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargi tare da kayayyakin da aka ƙwato ga manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Gusau.
Ya ce wannan nasara ta biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa wata mota mai ɗauke da kaya ta tashi daga Danhasiya Plaza da ke Gusau zuwa ƙauyen Bindin, yankin da ake zargin yana ƙarƙashin ikon ’yan bindiga.
A cewarsa, jami’an sun tare motar mai lamba KMC 120-XR, inda suka kama direban tare da wasu mutane shida kuma ayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da kuɗi Naira miliyan 13,352,500, abubuwan fashewa 98 na na’urorin gargajiya (IEDs) da ake zargin dynamite ne, na’urorin tayar da fashewa guda 25, babura sababbi guda uku, wayoyin Android, sigari, ’ya’yan itacen tuffa, jarkoki huɗu na dizal, jarkoki uku na man ja, da kuma kayan haƙa kamar felaye da cokula.
Dalijan ya ce za a miƙa waɗanda aka kama tare da kayayyakin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.
A cikin bayaninsa, direban motar, Abubakar Abdullahi Dangulbi, ya ce wani mai suna Aliyu Labaran ne ya ɗauke shi aiki domin kai kuɗin ga wani Alhaji Abubakar Bindin daga hannun wani Nasiru Dan Zuru (wanda ke tsere), yayin da aka ce na’urorin fashewar na wani Jamilu Lingyado ne a ƙauyen Bindin, Sai kuma yace bai san abin da ke cikin kayan ba, yana mai jaddada cewa shi aikin kai saƙo kawai aka ba shi.
“Ban san abin da ke cikin kayan ba. An ba ni aikin kai su ne kawai ga masu su a Bindin,” in ji shi.
Dalijan ya yi gargaɗi cewa matsalar tsaro da ke addabar jihar Zamfara na samun ƙarfi ne daga masu haɗin gwiwa da ke samar wa ’yan bindiga kayan aiki, bayanan sirri da sauran tallafi, ya kuma jaddada cewa irin waɗannan na’urorin fashewa na iya jawo asarar rayuka masu yawa ga fararen hula da jami’an tsaro.
Ya ƙara da cewa rundunar CPG za ta ci gaba da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu aikata laifuka, tare da tabbatar da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Haka kuma, ya yaba wa gwamnatin jihar Zamfara kan tallafin kayan aiki da take bayarwa, yana mai cewa za a yi amfani da su yadda ya kamata wajen yaƙi da ’yan bindiga.
Wannan nasara ta ƙara nuna damuwa a tsakanin masana harkar tsaro cewa matsalar ’yan bindiga a Zamfara na ƙara samun goyon baya ta hanyar tsare-tsaren samar da kayayyaki masu ƙarfi, lamarin da ke buƙatar ƙarin tsauraran matakan sa ido da kuma katse hanyoyin samar da irin waɗannan kayayyaki.


