2027: Tsohon Gwamnan Bauchi, da ke Najeriya ya sayi takardan cikewa don yin takarar gwamna a APC
Daga Ahmad Muhammad, Bauchi
Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi Mohammed Abdullahi Abubakar ya sayi takardan cikewa ɗin nuna sha’awa da tsayawa takara na muqamin Gwamna a Jam’iyyar APC don tsayawa takarar gwamnan Jihar Bauchi a zaven 2027..
Dan takarar Abubakar ya ce matakin ya nuna jajircewarsa ga tsarin da jam’iyyar ta shimfida da kuma ƙa’idodin dimokuraɗiyya na cikin gida.
Abubakar ya ce: “Wannan matakin yana nuna bin ka’ida da na yi wa tsarin jam’iyyar da aka kafa da kuma imanina mara yankewa game da tsarin dimokuradiyya na cikin gida na APC.
“Kamar yadda yawancin masu ruwa da tsaki na APC suka ce, ina sake nanata cikakken goyon bayana ga matsayin jam’iyyar kan amincewa da ko dai kuri’un da aka kaxa ko kuma na zaven fidda gwani kai tsaye, amma saboda hanyar data fi shine idan aka samu daidaito aka cimma matsaya wajen zavar ‘xan takarar gwamna, zai taimaka wajen inganta hadin kan cikin gida, rage tsadar kashe kuxi wajen zaven fidda Gwani,da qalubalen dabaru na zaben fidda gwani kai tsaye, da kuma rage barazanar rashin gaisuwa, da kai qara da shari’a da sauya sheqa daga masu neman takara da suka fusata saboda yana samar da “’yan takara masu dacewa ta hanyar daidaita ra’ayin jama’a,
Ya yi kira ga masu fafatawa da su haxu su amince da mutum daya, jam’iyyar da nufin neman hana rabuwar kawuna bayan zaven fidda gwani, tare da tabbatar da hadin kan jam’iyya kamar yadda mafi yawansu suka nuna sha’awa.
“Ina da yaqinin cewa wannan hanyar za ta kara zurfafa dimokuradiyya ta qarfafa hadin kan jam’iyya, da kuma bai wa kowane memba damar jin cewa shi ne wanda ya tsaida xan takarar a lokacin fitowar ‘yan takara,” in ji shi.
Ya kuma sake nanata amincinsa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma shugabancin jam’iyyar a matakin qasa da jiha.
“Ina sake nanata girmamawata, biyayyata, da kuma jajircewara mara yankewa ga Shugaban Jam’iyyar APC na qasa kuma Shugaba Bola Tinubu.
“Haka nan ina mika gaisuwata ga shugabannin jam’iyyar a Jihar Bauchi, manyan dattawanta, da dukkan shugabannin da aka san su waɗanda jagorancinsu ke ci gaba da tsara manufofin ci gaba na APC,” in ji shi.
Dan takarar gwamna ya yaba wa masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da magoya bayansu saboda goyon bayansu kuma ya yi alƙawarin aiwatar da ayyukan da Zai kyautata rayuwar al’umma Idan yayi nasarar zaɓensa a matsayin Gwamnan Jihar na gaba.
Abubakar ya kammala wa’adinsa na farko kuma ya sha kaye a zaɓen a 2019, yanzu yana son dawowa don kammala wa’adinsa na biyu na zaɓe.
Yawan ‘yan takarar da suka sayi tikitin takarar Gwamna na APC daga Bauchi yanzu su ne Shehu Buba , Yusuf Tuggar, da tsohon Gwamna Mohammed Abdullahi Abubakar. Sauran waxanda Basu saya ba ana Ganin akwai Ministan lafiya Ali Pate, Dokta Bala Wunti DA Nura Many Soro zuwa lokacin da muke haxa wannan rahoto


