Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna
Published: May 5, 2026 at 3:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A halin yanzu, direbobin baburan adaidaita sahu (keke Napep) a birnin Kaduna sun fara numfasawa biyo bayan rungumar amfani da iskar gas (CNG) wanda ya rage musu radadin tsadar man fetur tare da dawo musu da ribar da suka dade suna nema suka rasa.

Binciken da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya gudanar ya nuna cewa, masu baburan da yawa na tururuwar komawa amfani da gas din, musamman bayan da farashin fetur ya yi tashin gwauron zabi sakamakon janye tallafi a shekarar 2023. Wannan sauyi ya sa da dama daga cikin wadanda suka ajiye sana’ar saboda faduwa, suka koma bakin aiki.

Musa Abdullahi, mai shekaru 38 da ke sana’ar a yankin Tudun Wada, ya bayyana cewa sauya wa zuwa gas ya rage masa asarar kudi.

“A baya, ina kashe kusan N15,000 kullum wajen siyan fetur, har ma wani lokacin idan na koma gida bani da sauran komai. Amma yanzu da iskar gas, abin da nake kashewa bai wuce N2,000 zuwa N3,000 ba,” in ji shi.

Haka shi ma Bala Garba, wanda ke bin hanyar Kawo, ya shaida wa NAN cewa a mako guda yana kashe N18,000 ne kawai a kan gas, sabanin N70,000 da yake babbakawa a baya.

“Dā ma idan na cire kudin mai da na gyara, N20,000 kawai nake tashi da ita a mako. Amma yanzu ina samun tsakanin N45,000 zuwa N50,000.”

Sani Lawal mai shekaru 32, ya ce lissafinsa na wata-wata ya canja. Yayin da dā yake kashe sama da N200,000 a wata wajen man fetur, yanzu da N75,000 kacal yake gudanar da harkokinsa, wanda hakan ke ba shi damar kai wa iyalinsa sama da N100,000 a karshen wata.

Wannan al’amari bai tsaya ga direbobin kadai ba, har ma da fasinjoji. Malama Amina Sule ta bayyana cewa wasu direbobin sun fara rage kudin mota.

“Hanyar da nake biyan N300 dā, yanzu ana dauka ta a kan N200 ko N250. Ko da yake ragi ne kadan, amma ya taimaka mana kwarai.”

Duk da wannan garabasa, masu ruwa da tsaki da kwararru a fannin sufuri sun nuna cewa akwai sauran rina a kaba. Babban abin damuwar masu adaidaita sahun shi ne karancin wuraren sayar da iskar gas din (CNG stations) da kuma tsadar sayen sabbin baburan masu amfani da gas.

Sai dai masana muhalli sun kara da cewa, amfani da iskar gas din ba riba kadai ba ne, yana kuma taimakawa wajen rage gurbatar iska a birane tunda gas din ba ya fitar da hayaki mai guba kamar fetur.

A karshe, Ibrahim Sadiq mai shekaru 27, wanda ya kusa barin sana’ar a shekarar 2025 saboda fatara, ya ce yanzu ya dawo sabon mutum. A cewarsa, idan aka dore a haka, za su iya dogaro da kansu yadda ya kamata.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
An Harbo Jirgin Yakin Amurka A Iran Amurka
Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.