Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna
Published: May 5, 2026 at 3:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A halin yanzu, direbobin baburan adaidaita sahu (keke Napep) a birnin Kaduna sun fara numfasawa biyo bayan rungumar amfani da iskar gas (CNG) wanda ya rage musu radadin tsadar man fetur tare da dawo musu da ribar da suka dade suna nema suka rasa.

Binciken da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya gudanar ya nuna cewa, masu baburan da yawa na tururuwar komawa amfani da gas din, musamman bayan da farashin fetur ya yi tashin gwauron zabi sakamakon janye tallafi a shekarar 2023. Wannan sauyi ya sa da dama daga cikin wadanda suka ajiye sana’ar saboda faduwa, suka koma bakin aiki.

Musa Abdullahi, mai shekaru 38 da ke sana’ar a yankin Tudun Wada, ya bayyana cewa sauya wa zuwa gas ya rage masa asarar kudi.

“A baya, ina kashe kusan N15,000 kullum wajen siyan fetur, har ma wani lokacin idan na koma gida bani da sauran komai. Amma yanzu da iskar gas, abin da nake kashewa bai wuce N2,000 zuwa N3,000 ba,” in ji shi.

Haka shi ma Bala Garba, wanda ke bin hanyar Kawo, ya shaida wa NAN cewa a mako guda yana kashe N18,000 ne kawai a kan gas, sabanin N70,000 da yake babbakawa a baya.

“Dā ma idan na cire kudin mai da na gyara, N20,000 kawai nake tashi da ita a mako. Amma yanzu ina samun tsakanin N45,000 zuwa N50,000.”

Sani Lawal mai shekaru 32, ya ce lissafinsa na wata-wata ya canja. Yayin da dā yake kashe sama da N200,000 a wata wajen man fetur, yanzu da N75,000 kacal yake gudanar da harkokinsa, wanda hakan ke ba shi damar kai wa iyalinsa sama da N100,000 a karshen wata.

Wannan al’amari bai tsaya ga direbobin kadai ba, har ma da fasinjoji. Malama Amina Sule ta bayyana cewa wasu direbobin sun fara rage kudin mota.

“Hanyar da nake biyan N300 dā, yanzu ana dauka ta a kan N200 ko N250. Ko da yake ragi ne kadan, amma ya taimaka mana kwarai.”

Duk da wannan garabasa, masu ruwa da tsaki da kwararru a fannin sufuri sun nuna cewa akwai sauran rina a kaba. Babban abin damuwar masu adaidaita sahun shi ne karancin wuraren sayar da iskar gas din (CNG stations) da kuma tsadar sayen sabbin baburan masu amfani da gas.

Sai dai masana muhalli sun kara da cewa, amfani da iskar gas din ba riba kadai ba ne, yana kuma taimakawa wajen rage gurbatar iska a birane tunda gas din ba ya fitar da hayaki mai guba kamar fetur.

A karshe, Ibrahim Sadiq mai shekaru 27, wanda ya kusa barin sana’ar a shekarar 2025 saboda fatara, ya ce yanzu ya dawo sabon mutum. A cewarsa, idan aka dore a haka, za su iya dogaro da kansu yadda ya kamata.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.