Mummunan lamari na kisan mutane da lalata dukiyoyi a jihar Filato ya kasance da matukar damuwa ga al’ummar jihar dake hankoron samun mafita.
Rahoton da wani komiti da gwamnatin jihar Filato ta kafa a shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, karkashin shugabancin Janar Nicholas Rogers ya bayyana cewa daga shekara ta dubu biyu da daya zuwa shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, mutane dubu goma sha daya da dari bakwai da arba’in da tara ne suka rasa ransu, dalilin rikice-rikicen da suka shafi neman wawure filin zama, da na noma da kiwo, ayyukan ‘yan bindiga da bata gari, rikice-rikicen da ake dangantawa da addini da kabilanci da sauransu.
Rahoton yace lamarin ya shafi yankuna dari hudu da ishirin a kananan hukumomi goma sha uku na jihar.
Tun bayan mika rahoton wa gwamnatin jihar Filato, al’ummar jihar, musamman wadanda ke karkara, sun ci gaba da samun kansu cikin wannan mummunan yanayi ba tare da sassauci ba.
A baya-bayan nan, wani lamari dake nema zama ruwan dare a wassu sassan jihar shine yadda matasa ke tare hanya, bayan kaiwa hari a kauye, cikin fushi su kashe ko jikkata matafiya da basu san hawa da sauka ba.
Mai fashin baki kan lamura, musamman a kafar sada zumunta, Steve Davou Damar yace babu addini ko dabi’a da ta goyi bayan kisan wanda bashi da laifi.
Shima shugaban rikon kwarya na gamayyan kungiyoyin matasa a Najeriya, Barista Buhari Ibrahim Shehu yace rashin sanin doka a bangaren matasa na daga dalilan da yasa batun tare hanya a kashe mutane ke ci gaba da aukuwa.
A bangare guda kuwa gwamnatin jihar Filato ta sha alwashin daukan mataki kan duk wanda ya tare hanya da sunan ramako.
Sakataren gwamnatin jihar Filato, Samuel Jatau yace wannan salo da al’ummar Filato ke yi na tare matafiya a kan hanyar gwamnati ba daidai bana, kuma gwamnatin zata dauki mataki.
Duk da shike wannan ba shine karo na farko da gwamnatin ke ikirarin daukan mataki ba, domin a kwanakin baya an jiyo gwamnan jihar Caleb Mutfwang na ikirarin kama duk wani basarake da matasan yankinsa suka tare hanya, to sai dai ko gwamnatin ta kama wani ko a’a, salon tare hanya da keyi a wassu sassan jihar na neman zama nomal, bi ma’ana, lamari na yau da kullum.
Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


