Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato
Published: May 8, 2026 at 12:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 8, 2026

Mummunan lamari na kisan mutane da lalata dukiyoyi a jihar Filato ya kasance da matukar damuwa ga al’ummar jihar dake hankoron samun mafita.

Rahoton da wani komiti da gwamnatin jihar Filato ta kafa a shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, karkashin shugabancin Janar Nicholas Rogers ya bayyana cewa daga shekara ta dubu biyu da daya zuwa shekara ta dubu biyu da ishirin da biyar, mutane dubu goma sha daya da dari bakwai da arba’in da tara ne suka rasa ransu, dalilin rikice-rikicen da suka shafi neman wawure filin zama, da na noma da kiwo, ayyukan ‘yan bindiga da bata gari, rikice-rikicen da ake dangantawa da addini da kabilanci da sauransu.

Rahoton yace lamarin ya shafi yankuna dari hudu da ishirin a kananan hukumomi goma sha uku na jihar.

Tun bayan mika rahoton wa gwamnatin jihar Filato, al’ummar jihar, musamman wadanda ke karkara, sun ci gaba da samun kansu cikin wannan mummunan yanayi ba tare da sassauci ba.

A baya-bayan nan, wani lamari dake nema zama ruwan dare a wassu sassan jihar shine yadda matasa ke tare hanya, bayan kaiwa hari a kauye, cikin fushi su kashe ko jikkata matafiya da basu san hawa da sauka ba.

Mai fashin baki kan lamura, musamman a kafar sada zumunta, Steve Davou Damar yace babu addini ko dabi’a da ta goyi bayan kisan wanda bashi da laifi.

Shima shugaban rikon kwarya na gamayyan kungiyoyin matasa a Najeriya, Barista Buhari Ibrahim Shehu yace rashin sanin doka a bangaren matasa na daga dalilan da yasa batun tare hanya a kashe mutane ke ci gaba da aukuwa.

A bangare guda kuwa gwamnatin jihar Filato ta sha alwashin daukan mataki kan duk wanda ya tare hanya da sunan ramako.

Sakataren gwamnatin jihar Filato, Samuel Jatau yace wannan salo da al’ummar Filato ke yi na tare matafiya a kan hanyar gwamnati ba daidai bana, kuma gwamnatin zata dauki mataki.

Duk da shike wannan ba shine karo na farko da gwamnatin ke ikirarin daukan mataki ba, domin a kwanakin baya an jiyo gwamnan jihar Caleb Mutfwang na ikirarin kama duk wani basarake da matasan yankinsa suka tare hanya, to sai dai ko gwamnatin ta kama wani ko a’a, salon tare hanya da keyi a wassu sassan jihar na neman zama nomal, bi ma’ana, lamari na yau da kullum.

Daga Jos Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/05/AUD-20260508-WA0035.mp3
Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu
Next Post: Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata

Karin Labarai Masu Alaka

Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
  • Magoya Bayan Tijjaniyya Zasu Kauracewa Zabe Saboda Kama Sheikh Sani Khalifa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.