Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata
Published: May 8, 2026 at 5:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: May 8, 2026

Gwamnatin jihar Kano a Najeriya ta kafa wani kwamitin mutum 12 domin dawo da naira biliyan 1.8 da aka ce an cire ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan gwamnati ta hannun kamfanonin bada lamuni masu zaman kansu.

Haka kuma gwamnatin ta dakatar da duk wata sabuwar yarjejeniyar rance tsakanin ma’aikatan gwamnati da kamfanonin lamunin, tana mai cewa daga yanzu ba za ta ƙara shiga tsakani a irin waɗannan yarjejeniyoyi ba.

Sakataren Gwamnatin Jiha, Umar Faruq Ibrahim, ya bayyana cewa wani bincike mai zaman kansa ya gano yadda wasu kamfanonin bada lamuni ke cire kuɗi daga albashin ma’aikata fiye da yadda doka ta tanada.

A cewarsa, dokar ta amince ne kada a cire fiye da kaso ɗaya bisa uku na albashin ma’aikaci, amma binciken ya nuna an karya wannan ƙa’ida.

Ya ce Majalisar Zartarwar Jihar ta amince da rahoton binciken tare da bai wa kwamitin da Kwamishinan Kuɗi, Ismaila Aliyu Danmaraya, ke jagoranta umarnin gano duk ma’aikatan da lamarin ya shafa, ko suna raye ko sun rasu, domin mayar musu da kuɗaɗensu.

SSG ɗin ya kuma bayyana cewa binciken ya wanke tsohon Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Abdullahi Musa, daga zargin hannu a badakalar.

Ya ƙara da cewa tun farko an yi kuskuren bayyana cewa kuɗin da suka ɓace sun kai naira biliyan 1.5, sai dai binciken ya tabbatar da cewa adadin ya kai naira biliyan 1.8.

Gwamnatin ta kuma nuna damuwa kan yadda ma’aikata ke ci gaba da karɓar lamuni daga kamfanoni masu zaman kansu, inda ta bayyana cewa jimillar bashin da ake bin ma’aikatan gwamnati a yanzu ya kai kusan naira biliyan 13.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato
Next Post: Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan-Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Daliban St. Mary! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
  • Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Matsayar Iran Na Kera Makamin Nuclear Bazai Sanja Ba Afrika
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.