Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Ta Dala Miliyan 428 A Abuja
Gwamnatocin ƙasashen Najeriya da Jamus sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar haɗin gwiwa ta bunkasa tattalin arziki da zuba jari ta miliyoyin daloli, da nufin ciyar da muhimman sassa gaba a fadin kasar.
Yarjejeniyar, wadda aka ƙiyasta ƙimarta a kan dalar Amurka miliyan 428, an kulla ta ne a birnin tarayya Abuja, inda ta mayar da hankali kan tallafawa fannonin makamashi, aikin gona, kiwon lafiya, da bunkasa dabarun dogaro da kai.
Haka zalika, tallafin zai shafi bunkasa kamfanoni masu zaman kansu domin samar da ayyukan yi.
Muhimman Abubuwan Da Yarjejeniyar Ta Kunsa:
1. Makamashi da Lantarki: Karfafa sauye-sauyen da ake yi a bangaren wutar lantarki a Najeriya.
2. Aikin Gona da Kiwon Lafiya: Kyautata harkar abinci da samar da ingantaccen tsarin lafiya.
3. Masana’antu: Tallafawa tsare-tsaren Najeriya na fadada masana’antu da kasuwanci.
Jami’an gwamnatin Jamus sun bayyana cewa wannan yarjejeniya babban mataki ne da zai tabbatar da zuba jari na dogon lokaci, tare da karfafa dankon zumuncin kasuwanci tsakaninsu da Najeriya, wadda ita ce kasa mafi karfin tattalin arziki a fadin nahiyar Afirka.


