Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa
Published: May 19, 2026 at 10:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar ‘yan yiwa Ƙasa Hidima ta Najeriya, National Youth Service Corps, ta bayyana cewa daga yanzu za ta riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima ne kawai idan sun gabatar da takardar shaidar tantancewa daga Nigeria Education Repository and Databank.

Babban Daraktan hukumar, Birgediya Janar Olakunle Nafiu, ne ya sanar da hakan yayin taron shirin tura masu yi wa ƙasa hidima na rukuni na “B” na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.

Ya ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Najeriya na daƙile amfani da jabun takardun kammala karatu tare da tabbatar da cewa sahihan waɗanda suka kammala karatu ne kawai ake bai wa damar gudanar da bautar ƙasa.

Janar Nafiu ya yi kira ga jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi masu fitar da ɗalibai zuwa bautar ƙasa da su ƙara wayar da kan ɗalibansu kan muhimmancin bin sabon tsarin tare da tabbatar da cikakken aiwatar da shi.

A cewarsa, aikin tantancewa da tura masu yi wa ƙasa hidima ba nauyin NYSC kaɗai ba ne, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin ilimi, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gaskiya, inganci da amincin tsarin bautar ƙasa.

Tun da farko, Daraktar Sashen Tura Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta NYSC, Misis Rachel Ideawor, ta bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da cibiyoyin ilimi domin inganta tsarin tura masu yi wa ƙasa hidima a faɗin ƙasar.

Ta kuma buƙaci jami’an kula da harkokin ɗalibai su gudanar da aikinsu cikin gaskiya da riƙon amana tare da tabbatar da cewa bayanan da ake aikawa sun dace da ainihin bayanan masu shirin bautar ƙasa.

Taron ya samu halartar wakilai daga Joint Admissions and Matriculation Board, National Universities Commission, National Board for Technical Education, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar ilimi da bautar ƙasa a Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito
Next Post: Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara

Karin Labarai Masu Alaka

Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
Masu Hakar Ma’adanai 37 Sun Mutu A Jihar Filato Bidiyo
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
  • Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba Amurka
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.