Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa
Published: May 19, 2026 at 10:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar ‘yan yiwa Ƙasa Hidima ta Najeriya, National Youth Service Corps, ta bayyana cewa daga yanzu za ta riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima ne kawai idan sun gabatar da takardar shaidar tantancewa daga Nigeria Education Repository and Databank.

Babban Daraktan hukumar, Birgediya Janar Olakunle Nafiu, ne ya sanar da hakan yayin taron shirin tura masu yi wa ƙasa hidima na rukuni na “B” na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.

Ya ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Najeriya na daƙile amfani da jabun takardun kammala karatu tare da tabbatar da cewa sahihan waɗanda suka kammala karatu ne kawai ake bai wa damar gudanar da bautar ƙasa.

Janar Nafiu ya yi kira ga jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi masu fitar da ɗalibai zuwa bautar ƙasa da su ƙara wayar da kan ɗalibansu kan muhimmancin bin sabon tsarin tare da tabbatar da cikakken aiwatar da shi.

A cewarsa, aikin tantancewa da tura masu yi wa ƙasa hidima ba nauyin NYSC kaɗai ba ne, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin ilimi, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gaskiya, inganci da amincin tsarin bautar ƙasa.

Tun da farko, Daraktar Sashen Tura Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta NYSC, Misis Rachel Ideawor, ta bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da cibiyoyin ilimi domin inganta tsarin tura masu yi wa ƙasa hidima a faɗin ƙasar.

Ta kuma buƙaci jami’an kula da harkokin ɗalibai su gudanar da aikinsu cikin gaskiya da riƙon amana tare da tabbatar da cewa bayanan da ake aikawa sun dace da ainihin bayanan masu shirin bautar ƙasa.

Taron ya samu halartar wakilai daga Joint Admissions and Matriculation Board, National Universities Commission, National Board for Technical Education, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar ilimi da bautar ƙasa a Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito
Next Post: Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
Shugaban Amurka Yace Zayyi Wahala A Cimma Yarjejeniya Tsakanin Isra’ila, Amurka Da Iran Amurka
Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Ansamu Girgizar Kasa A Kasar Taiwan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.