Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani na Najeriya, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya sanar da janyewarsa daga zaben fidda gwani na kujerar gwamnan jihar Gombe karkashin jam’iyyar All Progressives Congress APC.
A cikin wata sanarwa da Barista Ibrahim M. Attahir ya fitar a madadin kungiyar Pantamiyya Movement a ranar 19 ga Mayun 2026, Pantami ya ce ya dauki matakin ne domin nuna rashin amincewa da abin da ya kira karya dokar zabe ta 2026 da kuma rashin samar da ingantaccen tsarin gudanar da zaben fidda gwani.
Sanarwar ta ce Pantami ya shiga takarar ne bayan kiraye-kirayen da ya samu daga matasa, mata, shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki a jihar, inda ya bi dukkan sharudda da ka’idojin jam’iyyar APC.
Ta kara da cewa Pantami ne kadai cikin masu neman takarar gwamna a APC da ya tura wakili zuwa taron yarjejeniyar zaman lafiya da Nigeria Police Force reshen jihar Gombe ya shirya ranar 14 ga Mayun 2026, kuma wakilinsa ne kadai ya sanya hannu kan yarjejeniyar.
Sai dai sanarwar ta zargi shugabannin jam’iyyar da kin bayar da muhimman bayanai dangane da yadda za a gudanar da zaben fidda gwani, ciki har da wuraren kada kuri’a, tsarin tantance wakilai da masu sa ido, da cibiyoyin tattara sakamako.
Pantami ya kuma yi zargin cewa zabukan fidda gwani na ‘yan majalisar tarayya da APC ta gudanar a ranakun 16 da 18 ga Mayun 2026 ba su bi ka’idojin dimokuradiyya ba, yana mai cewa an ware ‘ya’yan jam’iyyar na kasa musamman matasa da mata daga tsarin zaben.
Sanarwar ta ce duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci, ba a aiwatar da wadannan umarni yadda ya kamata ba a jihar Gombe.
Pantami ya gode wa matasa da suka hada kudade domin sayen fom dinsa na nuna sha’awa da takara, inda gudummawar ta kai daga naira dubu biyar zuwa miliyan hudu, tare da bayyana cewa an gudanar da komai a fili.
Ya kuma yaba wa magoya bayansa, musamman matasa da mata, da masu ruwa da tsaki daga mazabu, kananan hukumomi da daukacin jihar Gombe bisa goyon baya da hadin kai.
A karshe, Pantami ya bukaci mabiyansa da su kasance masu bin doka da oda tare da tabbatar da zaman lafiya a jihar, yana mai cewa kungiyar Pantamiyya za ta sanar da matakinta na gaba nan gaba kadan.


