Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara
Published: May 19, 2026 at 7:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani na Najeriya, Isa Ali Ibrahim Pantami, ya sanar da janyewarsa daga zaben fidda gwani na kujerar gwamnan jihar Gombe karkashin jam’iyyar All Progressives Congress APC.

A cikin wata sanarwa da Barista Ibrahim M. Attahir ya fitar a madadin kungiyar Pantamiyya Movement a ranar 19 ga Mayun 2026, Pantami ya ce ya dauki matakin ne domin nuna rashin amincewa da abin da ya kira karya dokar zabe ta 2026 da kuma rashin samar da ingantaccen tsarin gudanar da zaben fidda gwani.

Sanarwar ta ce Pantami ya shiga takarar ne bayan kiraye-kirayen da ya samu daga matasa, mata, shugabanni da sauran masu ruwa da tsaki a jihar, inda ya bi dukkan sharudda da ka’idojin jam’iyyar APC.

Ta kara da cewa Pantami ne kadai cikin masu neman takarar gwamna a APC da ya tura wakili zuwa taron yarjejeniyar zaman lafiya da Nigeria Police Force reshen jihar Gombe ya shirya ranar 14 ga Mayun 2026, kuma wakilinsa ne kadai ya sanya hannu kan yarjejeniyar.

Sai dai sanarwar ta zargi shugabannin jam’iyyar da kin bayar da muhimman bayanai dangane da yadda za a gudanar da zaben fidda gwani, ciki har da wuraren kada kuri’a, tsarin tantance wakilai da masu sa ido, da cibiyoyin tattara sakamako.

Pantami ya kuma yi zargin cewa zabukan fidda gwani na ‘yan majalisar tarayya da APC ta gudanar a ranakun 16 da 18 ga Mayun 2026 ba su bi ka’idojin dimokuradiyya ba, yana mai cewa an ware ‘ya’yan jam’iyyar na kasa musamman matasa da mata daga tsarin zaben.

Sanarwar ta ce duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na gudanar da sahihin zabe na gaskiya da adalci, ba a aiwatar da wadannan umarni yadda ya kamata ba a jihar Gombe.

Pantami ya gode wa matasa da suka hada kudade domin sayen fom dinsa na nuna sha’awa da takara, inda gudummawar ta kai daga naira dubu biyar zuwa miliyan hudu, tare da bayyana cewa an gudanar da komai a fili.

Ya kuma yaba wa magoya bayansa, musamman matasa da mata, da masu ruwa da tsaki daga mazabu, kananan hukumomi da daukacin jihar Gombe bisa goyon baya da hadin kai.

A karshe, Pantami ya bukaci mabiyansa da su kasance masu bin doka da oda tare da tabbatar da zaman lafiya a jihar, yana mai cewa kungiyar Pantamiyya za ta sanar da matakinta na gaba nan gaba kadan.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa
Next Post: Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani

Karin Labarai Masu Alaka

Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
  • ‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
  • Tsofin Ma’aikatan Gwamnati Sunyi Zanga Zanga A Jihar Neja Labarai
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.