Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
Published: June 3, 2026 at 5:02 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mahukuntan Iran sun sanar da shirye-shiryen gudanar da jana’izar tsohon Jagoran Addini na kasar, Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya rasu yana da shekaru 86 a duniya.

A cewar jami’an kasar, za a gudanar da jana’izar ne a manyan biranen Tehran, Qom da Mashhad cikin wani shiri na kwanaki uku da aka tanada domin bai wa miliyoyin ‘yan Iran da masu biyayya daga sassa daban-daban na duniya damar yi masa bankwana na karshe.

Rahotanni sun bayyana cewa za a fara gudanar da manyan tarukan addu’o’i da zaman makoki a Tehran, babban birnin kasar, inda ake sa ran miliyoyin mutane za su hallara domin girmama marigayin wanda ya jagoranci Iran na tsawon shekaru fiye da talatin. Jami’ai sun ce faretin jana’izar a Tehran kadai zai dauki akalla sa’o’i 24 saboda yawan mahalarta da ake tsammani.

Bayan kammala bukukuwan da za a yi a Tehran, za a ci gaba da jana’izar a birnin Qom, wanda ake kallonsa a matsayin cibiyar ilimin addinin Shi’a a Iran. Daga nan ne za a kai gawar zuwa Mashhad, garin haihuwarsa da ke arewa maso gabashin kasar, inda za a binne shi a Hubbaren Imam Reza bisa wasiyyarsa.

Mahukuntan Tehran sun ce mutane daga kasashe da dama, ciki har da Pakistan, Afghanistan, Indiya, Bangladesh da yankin Kashmir, na sa ran halartar jana’izar domin nuna girmamawa ga marigayin. Haka kuma, larduna daban-daban na Iran sun nemi damar karbar bakuncin tarukan makoki, lamarin da ke nuna irin tasirin da ya yi a fagen siyasa da addini.

Ana kallon wannan jana’iza a matsayin daya daga cikin mafi girman bukukuwan makoki da Iran za ta taba yi tun bayan jana’izar Ayatollah Ruhollah Khomeini a shekarar 1989, wadda ta jawo taron miliyoyin mutane daga sassa daban-daban na duniya.

Ali Khamenei ya kasance Jagoran Addinin Jamhuriyar Musulunci ta Iran tun daga shekarar 1989 har zuwa rasuwarsa, kuma mutuwarsa ta kawo karshen wani zamani mai muhimmanci a tarihin siyasar kasar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
Next Post: Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.