Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
Published: June 3, 2026 at 5:02 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mahukuntan Iran sun sanar da shirye-shiryen gudanar da jana’izar tsohon Jagoran Addini na kasar, Ayatollah Ali Khamenei, wanda ya rasu yana da shekaru 86 a duniya.

A cewar jami’an kasar, za a gudanar da jana’izar ne a manyan biranen Tehran, Qom da Mashhad cikin wani shiri na kwanaki uku da aka tanada domin bai wa miliyoyin ‘yan Iran da masu biyayya daga sassa daban-daban na duniya damar yi masa bankwana na karshe.

Rahotanni sun bayyana cewa za a fara gudanar da manyan tarukan addu’o’i da zaman makoki a Tehran, babban birnin kasar, inda ake sa ran miliyoyin mutane za su hallara domin girmama marigayin wanda ya jagoranci Iran na tsawon shekaru fiye da talatin. Jami’ai sun ce faretin jana’izar a Tehran kadai zai dauki akalla sa’o’i 24 saboda yawan mahalarta da ake tsammani.

Bayan kammala bukukuwan da za a yi a Tehran, za a ci gaba da jana’izar a birnin Qom, wanda ake kallonsa a matsayin cibiyar ilimin addinin Shi’a a Iran. Daga nan ne za a kai gawar zuwa Mashhad, garin haihuwarsa da ke arewa maso gabashin kasar, inda za a binne shi a Hubbaren Imam Reza bisa wasiyyarsa.

Mahukuntan Tehran sun ce mutane daga kasashe da dama, ciki har da Pakistan, Afghanistan, Indiya, Bangladesh da yankin Kashmir, na sa ran halartar jana’izar domin nuna girmamawa ga marigayin. Haka kuma, larduna daban-daban na Iran sun nemi damar karbar bakuncin tarukan makoki, lamarin da ke nuna irin tasirin da ya yi a fagen siyasa da addini.

Ana kallon wannan jana’iza a matsayin daya daga cikin mafi girman bukukuwan makoki da Iran za ta taba yi tun bayan jana’izar Ayatollah Ruhollah Khomeini a shekarar 1989, wadda ta jawo taron miliyoyin mutane daga sassa daban-daban na duniya.

Ali Khamenei ya kasance Jagoran Addinin Jamhuriyar Musulunci ta Iran tun daga shekarar 1989 har zuwa rasuwarsa, kuma mutuwarsa ta kawo karshen wani zamani mai muhimmanci a tarihin siyasar kasar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
Next Post: Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gidauniyar Jalo Wali Ta Ƙaddamar Da Bada Audugar Mata A Gombe Afrika
Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • An Yaba Wa Gwamnatin Bauchi Bisa Karban Bakuncin Gasar Polo Wasanni
  • Farashin Zinari Yayi Tashin Gwauron Zabi Amurka
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.