Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas
Published: June 30, 2026 at 6:25 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Masu ruwa da tsaki daga sassan yankin Arewa Maso Gabas sun yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma aiwatar da shirye-shiryen zaman lafiya da suka haɗa kowa da kowa domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a yankin.

An yi wannan kira ne a yayin taron kwana biyu na North-East Peace Mission Conference da Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) ta shirya a jihar Gombe.

Da yake jawabi a taron, Manajan Daraktan NEDC, Mohammed Alkali, ya bayyana cewa zaman lafiya mai ɗorewa shi ne ginshiƙin sake farfaɗo da yankin da kuma samar da ci gaba mai anfani ga al’umma.

Alkali, wanda Kodinetan NEDC na Jihar Gombe, Arc. Usman Muhammad, ya wakilta, ya ce an shirya taron ne domin ƙarfafa tattaunawa, bunƙasa haɗin kan al’umma da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin ci gaba, shugabannin al’umma da matasa.

Ya ce hukumar na ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen gina zaman lafiya a faɗin yankin Arewa Maso Gabas, inda ya bayyana cewa ayyukan da suka shafi gine-ginen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, samar da hanyoyin dogaro da kai da sake tsugunar da waɗanda rikice-rikice suka raba da muhallansu na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

A cewarsa, NEDC ta samu gagarumar nasara wajen sake gina al’ummomin da matsalar ta’addanci ta daidaita, ta hanyar samar da muhimman ababen more rayuwa, tallafa wa marasa galihu da kuma farfaɗo da harkokin tattalin arziki domin inganta rayuwar jama’a.

Yayin da yake gabatar da muƙala kan rawar da matasa za su taka wajen gina zaman lafiya, Mataimakin Farfesa a fannin Tarihin Soja da Nazarin Tsaro na Jami’ar Maiduguri, Dakta Abubakar Muhammad, ya jaddada muhimmancin bai wa matasa dama da goyon baya domin su kasance sahun gaba wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Ya buƙaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su ƙara zuba jari a ilimi, koyar da sana’o’i da kuma ƙarfafa matasa su shiga harkokin ci gaban al’umma. Haka kuma ya yi kira ga al’umma da su rungumi tare da tallafa wa sake haɗa tsoffin mayaƙan da suka ajiye makamai cikin jama’a a matsayin wani ɓangare na sulhu da farfaɗo da yankin.

Ɗaya daga cikin mahalarta taron, Yasin Idris, ya ce taron ya ba matasa damar bayyana ra’ayoyinsu tare da bayar da gudunmawa wajen samar da mafita ga matsalolin da ke addabar yankin.

Ya yi kira da a ƙara bai wa matasa dama su shiga ayyukan gina zaman lafiya ta hanyar shirye-shiryen wayar da kai, tattaunawa da ayyukan raya al’umma, yana mai nuna kwarin gwiwar cewa haɗin kai da shigar kowa da kowa za su taimaka wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa da ci gaba mai anfani a Arewa Maso Gabas.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi
Next Post: APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NAHCON Tafara Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 Najeriya
  • Sudan Takai Hari Kasar Chadi Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
  • An Yankewa Prime Ministan Kasar Tunisiya Hukuncin Shekaru 24 A Gidan Yari Afrika
  • Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.