Masu ruwa da tsaki daga sassan yankin Arewa Maso Gabas sun yi kira da a ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da kuma aiwatar da shirye-shiryen zaman lafiya da suka haɗa kowa da kowa domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a yankin.
An yi wannan kira ne a yayin taron kwana biyu na North-East Peace Mission Conference da Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) ta shirya a jihar Gombe.
Da yake jawabi a taron, Manajan Daraktan NEDC, Mohammed Alkali, ya bayyana cewa zaman lafiya mai ɗorewa shi ne ginshiƙin sake farfaɗo da yankin da kuma samar da ci gaba mai anfani ga al’umma.
Alkali, wanda Kodinetan NEDC na Jihar Gombe, Arc. Usman Muhammad, ya wakilta, ya ce an shirya taron ne domin ƙarfafa tattaunawa, bunƙasa haɗin kan al’umma da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, ƙungiyoyin ci gaba, shugabannin al’umma da matasa.

Ya ce hukumar na ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen gina zaman lafiya a faɗin yankin Arewa Maso Gabas, inda ya bayyana cewa ayyukan da suka shafi gine-ginen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, samar da hanyoyin dogaro da kai da sake tsugunar da waɗanda rikice-rikice suka raba da muhallansu na taimakawa wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
A cewarsa, NEDC ta samu gagarumar nasara wajen sake gina al’ummomin da matsalar ta’addanci ta daidaita, ta hanyar samar da muhimman ababen more rayuwa, tallafa wa marasa galihu da kuma farfaɗo da harkokin tattalin arziki domin inganta rayuwar jama’a.
Yayin da yake gabatar da muƙala kan rawar da matasa za su taka wajen gina zaman lafiya, Mataimakin Farfesa a fannin Tarihin Soja da Nazarin Tsaro na Jami’ar Maiduguri, Dakta Abubakar Muhammad, ya jaddada muhimmancin bai wa matasa dama da goyon baya domin su kasance sahun gaba wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Ya buƙaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su ƙara zuba jari a ilimi, koyar da sana’o’i da kuma ƙarfafa matasa su shiga harkokin ci gaban al’umma. Haka kuma ya yi kira ga al’umma da su rungumi tare da tallafa wa sake haɗa tsoffin mayaƙan da suka ajiye makamai cikin jama’a a matsayin wani ɓangare na sulhu da farfaɗo da yankin.
Ɗaya daga cikin mahalarta taron, Yasin Idris, ya ce taron ya ba matasa damar bayyana ra’ayoyinsu tare da bayar da gudunmawa wajen samar da mafita ga matsalolin da ke addabar yankin.
Ya yi kira da a ƙara bai wa matasa dama su shiga ayyukan gina zaman lafiya ta hanyar shirye-shiryen wayar da kai, tattaunawa da ayyukan raya al’umma, yana mai nuna kwarin gwiwar cewa haɗin kai da shigar kowa da kowa za su taimaka wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa da ci gaba mai anfani a Arewa Maso Gabas.


