Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa
Published: November 29, 2025 at 8:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 29, 2025

Kamfanin Orano ya sanar cewa hukumomn Nijar sun fara aiyukan fitar da ton ton na Uranium daga garin Arlit zuwa waje ba tare da sanar da shi ba. Matakin da kamfanin na Faransa ya ce ya saba wa umurnin kotun bankin duniya, wace ta bukaci bangarorin su jira ta kammala shari’ar da ke gabanta.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnatin Nijar  sai dai kwararru kan sha’anin ma’adanai sun fara bayyana matsayinsu.
A kalla ton 1300 na Uranium ne ke jibge a kamfanin SOMAIR da ke Arlit na arewacin Nijar bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da fitarwa zuwa waje a washegarin juyin mulkin Yulin 2023, saboda abin da suka kira rashin haske daga kamfanin Orano da ke harkar Uranium shekaru sama da 50.
Dangantaka ta ci gaba da tsami a tsakanin bangarorin biyu abin da ya sa Orano shigar da kara a kotun CIRDI domin ta shiga tsakani. A yayin da ake jiran matsayin kotun kamfanin na Faransa ya sanar cewa motoci dauke da lodin Uranium sun fara dagawa daga Arlit zuwa Agadez a yunkurin Isa gabar teku. Kwararre kan sha’anin albarkatun karkashin kasa Mahamadou Tchiroma Aissami na fassara abin a matsayin ci gaban takaddama.
Kamfanin na Orano ya ce fitar da Uranium a wannan lokaci ya saba wa umurnin kotu. sai dai ‘yan Nijar irinsu masani a harakar makamashi injiniya Rabiou Malan Issa na ganin koma mai ake ciki Nijar ce uwar gijiyar albarkatun da ake rikicin kan su.
 Nijar na daga cikin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjeniyoyin hakar ma’adanai da hanyoyin sayar da su a kasuwannin duniya, dalili kenan wadanda suka lakanci fannin ke gargadin mahukunta a kan hanyoyin mafita.
 Jamhuriyar Nijar na daga cikin kasashen da suka fi kowa yawan Uranium a duniya sai dai alamu na nunin kasar da al’ummarta ba su amfana da arzikin, kamar yadda ya dace abin da ya sa gwamnatin CNSP ta dage da yunkurin sabunta abokan hulda a wannan fanni kuma bayanai na cewa kamfanin ROSATOM na Russia na daga cikin masu fatan ganin an ba su dama.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed
Next Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!

Karin Labarai Masu Alaka

Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu Afrika
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba Afrika
Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.