Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da naɗin Manyan Sakatarori guda 19 don cike guraben aiki da ake da su a Ma’aikatun Gwamnatin Jihar da kuma ƙarfafa harkokin gudanarwa don samar da ayyuka masu inganci ga jama’a.
Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jiha, Farfesa Mu’azu Shehu, wanda ya sanar da amincewar Gwamnan, yace naɗin ya zama dole sakamakon rashin manyan Sakatarorin a ma’aikatu da dama, duba da ƙirƙira da sake fasalin wassu ma’aikatu da gwamnatin jihar ta yi kwanan nan.
Ya bayyana cewa cike guraben da aka rasa zai tabbatar da cewa ma’aikatun da abin ya shafa sun samu jagoranci mai inganci kuma sun samu kyakkyawan yanayin aiwatar da ayyukansu yadda ya kamata.
Farfesa Shehu yace an zaɓo jami’an da aka naɗan ne don daga ƙananan hukumomi 11, tare da la’akari da yankunansu daban-daban, da ƙwarewar aiki da kuma muhimman buƙatun ma’aikatun daban-daban.
Ya jaddada cewa naɗe-naɗen an yi su ne bisa dogara da dacewa, ƙwarewa da kuma bayanan da aka tabbatar na jami’an, yana mai cewa jami’an da aka naɗan sun gudanar da kyawawan ayyuka a duk tsawon ayyukansu kuma suna da kyakkyawan tarihin aikinsu mai tsabta.
A cewarsa, an tantance jami’an sosai kuma an ga sun dace da riƙon muƙaman, bayan sun samu gogewar data dace da kuma nuna jajircewa, ƙwarewa da azama a fannoni daban-daban na ayyukansu.
Ya ƙara da cewa ƙimar aikinsu mai gamsarwa da kuma tarihin aikinsu mai tsabta sune tushe mai ƙarfi na ɗaukaka su zuwa manyan sakatarorin.
Sabbin Manyan Sakatarorin da aka naɗa su ne:
Haruna Mohammed Danburam – daga Ƙaramar Hukumar Akko
Mohammed Auwal Ahmed – daga Ƙaramar Hukumar Akko
Alheri Yoriyo – daga Ƙaramar Hukumar Balanga
Haruna Bello Gelengu – daga Ƙaramar Hukumar Balanga
Ruth Caleb Maina – daga Ƙaramar Hukumar Billiri
Auwal Abduljalal – daga Ƙaramar Hukumar Dukku
Kasimu Umar – daga Ƙaramar Hukumar Dukku
Musa Muhammad Babaji – daga Ƙaramar Hukumar Funakaye
Adamu Audi, Esq. – daga Ƙaramar Hukumar Funakaye
Dr. Hadi Mohammed – daga Ƙaramar Hukumar Karamar Hukumar Gombe
Ali Yaya Ahmed – daga Ƙaramar Hukumar Karamar Hukumar Gombe
Kabiru Mohammed Mahdi – daga Ƙaramar Hukumar Kwami
Balarabe Musa – daga Ƙaramar Hukumar Kaltungo
Tabitha B. James – daga Ƙaramar Hukumar Kaltungo
Dr Haruna Dadum Hamza, daga Ƙaramar Hukumar Nafada
Ibrahim Mohammed Gombe – daga Ƙaramar Hukumar Nafaɗa
Tahir Adamu Sadiq – daga Ƙaramar Hukumar Shongom
Shuai’bu Chiroma Muhammad – daga Ƙaramar Hukumar Yamaltu-Deba
Musa Idi Batari – daga Ƙaramar Hukumar Yamaltu-Deba
Gwamna Inuwa Yahaya yana sa ran sabbin Manyan Sakatarorin za su yi amfani da tarin gogewa, ƙwarewa da sanin makamar aiki wajen sauƙe nauyin da aka ɗora musu, yayinda suke bada gudummawa mai ma’ana ga manufar gwamnati na gina ma’aikata masu nagarta, inganci da kuma kwarewa.
Duk naɗe-naɗen sun fara aiki ne nan take.


