Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Galatasaray Ta Yi Watsi Da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen
Published: August 20, 2026 at 5:41 PM | By: Bala Hassan

Galatasaray Ta Yi Watsi da Tayin €150m Daga Al-Hilal Kan Victor Osimhen

Kungiyar Galatasaray ta Turkiyya ta yi watsi da tayin da ya kai Yuro miliyan 150 daga Al-Hilal ta Saudiyya domin daukar dan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen.

A cewar rahoton BSN Sports, Al-Hilal ta nuna sha’awarta ta daukar Osimhen, wanda Galatasaray ta dauka daga Napoli a farkon kakar wasan da ta gabata.

Rahoton ya ce tawagar Saudiyya karkashin jagorancin Yarima Nawaf bin Saad ta fara da tayin baki na Yuro miliyan 130, inda yariman ya sanar da shugabannin Galatasaray cewa zai zo Istanbul da kansa idan tattaunawar ta zama ta hukuma.

Bayan haka, Al-Hilal ta yi wa Osimhen tayin albashin Yuro miliyan 50 a duk shekara, amma Galatasaray ta sanar da kungiyar Saudiyyar cewa ba ta da niyyar sayar da dan wasan.

Daga bisani Al-Hilal ta kara tayin zuwa Yuro miliyan 150, amma har yanzu shugaban Galatasaray, Dursun Özbek, da shugabannin kungiyar sun yi fatali da tayin, tare da bayyana aniyarsu ta ci gaba da rike dan wasan.

Osimhen, wanda rahoton ya ce yana matukar farin ciki a Galatasaray, ya kuma bayyana cewa abin da ya fi mayar da hankali a kai shi ne kakar wasa ta gaba, ba batun kudi ba.

Dan wasan na Najeriya ya kuma fara kakar gasar lig din Turkiyya da kyau, bayan ya zura kwallaye biyu a wasan makon farko da Çorum FK.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: NSC Ta Bai Wa Shugabannin NFF Sa’o’i 24 Su Yi Murabus
Next Post: Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa

Karin Labarai Masu Alaka

Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai Wasanni
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
  • Bana Ba Harka Ga ‘Yan-Wasan Kwallon Kafar Najeriya Wasanni
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.