Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu Afrika

APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye
Published: August 22, 2026 at 3:11 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Injiniya Dr. Usman Maijama’a Kallamu ya zama ɗan takarar jam’iyyar APC a zaɓen cike gurbin kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Gombe, Kwami da Funakaye.

An gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kwamitin Zaɓen, Dr. Habu Dahiru, Kwamishinan Kimiyya da Fasaha na Jihar Gombe, tare da halartar jami’an hukumomin zaɓe da suka sanya ido kan yadda aka gudanar da aikin.

Da yake gabatar da tsarin zaɓen, Dr. Habu Dahiru ya bayyana ƙa’idoji da matakan da za a bi wajen gudanar da zaɓen, kafin ya gabatar da wakilan jam’iyyar da aka tantance daga ƙananan hukumomin Gombe, Kwami da Funakaye waɗanda suka cancanci kaɗa kuri’a.

Daga nan ne aka ayyana Injiniya Dr. Usman Maijama’a Kallamu a matsayin wanda ya yi nasara ba tare da hamayya ba, bayan dukkan wakilan jam’iyyar APC da aka tantance daga ƙananan hukumomin uku sun amince da shi baki ɗaya.

A jawabinsa na karɓar takarar, Injiniya Dr. Usman Maijama’a Kallamu ya nuna godiya ga al’ummar mazabar bisa amincewar da suka nuna masa da kuma zaɓar sa domin ya wakilce su ƙarƙashin tutar jam’iyyar APC.

Ya yi kira ga sauran masu neman takarar da magoya bayansu da su haɗa kai tare da yin aiki tare domin ganin jam’iyyar APC ta samu nasara a dukkan matakai.

Tun da farko, Shugaban Ƙaramar Hukumar Kwami, Alhaji Ibrahim Buba Makama, ya yaba wa Kwamitin Zaɓen ƙarƙashin jagorancin Dr. Habu Dahiru bisa yadda ya gudanar da zaɓen fidda gwani cikin nasara.

Ya kuma yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki a mazabar bisa haɗin kai da jajircewar da suka nuna wajen tabbatar da gudanar da zaɓen cikin lumana da nasara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kannywood: Ali Nuhu Ya Shiga Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Tinubu
Next Post: Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba Afrika
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Chukwueze, Ya Ci Gaba Da Riƙe Rigarsa Mai Lamba 21 A AC Milan Wasanni
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Hafsan Sojin Najeriya: Samar Da Sabbin Wajen Horas Da Sojoji Zai Inganta Tsaro Tsaro
  • Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.