Rundunar ’Yan Sandan jihar Bauchi a Arewa Maso Gabashin Najeriya ta kama wani dattijo mai shekaru 70, Usman Abubakar, bisa zargin lalata da wata yarinya ’yar shekara takwas a yankin Tsakanin Bayara da ke cikin birnin Bauchi.
Mahaifin yarinyar, mai shekaru 48, ne ya kai rahoton lamarin ofishin ’yan sanda na ‘E’ Division da ke Yelwa.
Ya zargi Abubakar, wanda ke zaune a yankin, da jan hankalin ’yarsa zuwa wani ginin da ba a kammala ba a ranar Lahadi, 24 ga watan Agusta, inda ake zargin ya yi lalata da ita.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Nafiu Habib, ya bayyana cewa kama wanda ake zargin na daga cikin kokarin rundunar na dakile cin zarafin mata da yara da kuma sauran nau’o’in tashin hankali bisa jinsi.
Ya ce bayan samun rahoton, jami’an ’yan sandan sun gaggauta daukar mataki tare da cafke wanda ake zargin.
SP Habib ya ce yayin gudanar da tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa aikata laifin.
An garzaya da yarinyar zuwa asibitin ’yan sanda domin duba lafiyarta da kuma ba ta kulawar da ta dace.
Kwamishinan ’yan sandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yi Allah-wadai da lamarin, tare da tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta gudanar da cikakken bincike kan lamarin.


