Kafin bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya ta 2026, wata tawaga ta malaman Kirista ƙarƙashin jagorancin Fasto Dr. Yohanna Buru, Babban Mai Kula da Christian Evangelical and Life Intervention Ministry a Jihar Kaduna, ta ziyarci hedikwatar Najeriya ta Jama’atu Nasril Islam (JNI) da ke Kaduna, domin ƙarfafa alaƙar Kirista da Musulmi da kuma inganta zaman lafiya, fahimtar juna da haɗin kan ƙasa.
Tawagar ta ce ziyarar na daga cikin shirye-shiryen bikin Ranar Zaman Lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya, wadda ake gudanarwa a kowace shekara a ranar 21 ga Satumba.
Da yake jawabi yayin ziyarar, Fasto Dr. Yohanna Buru ya ce sun je hedikwatar JNI ne domin musayar saƙonnin fatan alheri da malaman Musulunci tare da ƙara ƙarfafa kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin Kiristoci da Musulmi a Arewacin Najeriya.
Ya ce ziyarar ta kuma mayar da hankali ne kan inganta zaman lafiya, fahimtar juna tsakanin mabiya addinai da haɗin gwiwa tsakanin al’ummomin addinai daban-daban.
Fasto Buru ya bayyana cewa ƙungiyarsa ta shirya gudanar da ayyuka na tsawon mako guda domin bikin Ranar Zaman Lafiya ta Duniya, ciki har da ziyartar asibitoci, al’ummomi, kasuwanni, makarantu, filayen wasa da sauran wuraren taruwar jama’a domin isar da saƙonnin zaman lafiya, haɗin kai da haƙurin addini.
Ya ce tattaunawa da shugabannin addinai daga ɓangarori daban-daban na da muhimmanci wajen gina amana da fahimtar juna a tsakanin al’umma.
Fasto Buru ya gode wa Sakataren-Janar na JNI, Farfesa Khalid Aliyu, bisa karɓar tawagar da kuma goyon bayan shirye-shiryen da ake yi na inganta zaman lafiya da haɗin kan al’umma.
Taken Ranar Zaman Lafiya ta Duniya ta 2026 shi ne: “Invest in Peace – For Everyone, Everywhere, Every Day”, wato “Zuba Jari a Zaman Lafiya – Ga Kowa, Ko’ina, Kowace Rana.”
A nasa jawabin, Sakataren-Janar na JNI, Farfesa Khalid Aliyu, ya yaba da ziyarar tare da jinjina wa Fasto Yohanna Buru kan ƙoƙarinsa na inganta zaman lafiya da haɗin kai a faɗin jihohin Arewa 19 na Najeriya.
Farfesa Khalid ya kuma yaba wa matasan malaman Kirista da suka raka Fasto Buru, yana mai cewa shigarsu cikin wannan yunƙuri na taimakawa wajen ƙarfafa fahimtar juna tsakanin mabiya addinai da zaman tare cikin lumana.
Ya yi kira ga ’yan Najeriya da su rungumi tattaunawa, mutunta juna da kuma warware saɓani cikin lumana domin gina al’umma mai haɗin kai.
Daga nan tawagar ta kuma ziyarci JNI reshen jihar Kaduna, inda ta gana da Imam Iliyasu Hussaini, Murshidin Jama’atu Nasril Islam na jihar Kaduna.
Imam Hussaini ya gode wa Fasto Buru da tawagarsa bisa ziyarar, yana mai cewa irin wannan yunƙuri na taimakawa wajen ƙarfafa kyakkyawar alaƙa tsakanin mabiya addinai a Kaduna da ma ƙasar baki ɗaya.
Ya yi kira ga shugabannin addinai da su ƙara himma wajen gudanar da addu’o’i da wayar da kan al’umma kan zaman lafiya, musamman yayin da ƙasar ke shirin tunkarar zaɓuka na gaba.
Imam Hussaini ya kuma buƙaci ’yan ƙasa da su guji daba da siyasa, shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da sauran ayyukan da ka iya kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron al’umma.
Ya ƙara jaddada buƙatar ’yan Najeriya su nuna kishin ƙasa tare da tallafa wa duk wani yunƙuri da ke inganta zaman lafiya, haɗin kai da zaman tare cikin lumana.
Tawagar ta ce za ta ci gaba da shirye-shiryen da aka tsara domin ƙarfafa gwiwar ’yan ƙasa, shugabannin addinai da al’ummomi wajen haɗa hannu domin gina al’adar zaman lafiya da haƙurin juna.


