Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya
Published: December 2, 2025 at 2:30 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 2, 2025

Shugaba Tinubu ya mika sunan Janar Christopher Musa domin zama Ministan Tsaron kasar.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya mika sunan tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa, ga majalisar dattawa domin tabbatar da shi a matsayin sabon Ministan Tsaro, bayan murabus da Alhaji Mohammed Badaru Abubakar yayi jiya.

A wata wasika da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, shugaba Tinubu ya ce nadin Janar Musa ya biyo bayan ajiye aiki da Badaru ya yi a ranar Litinin saboda matsalolin lafiya.

Janar Musa, mai shekaru 58 da haihuwa a ranar 25 ga Disamba, ya kasance ɗaya daga cikin manyan hafsoshin soja da suka yi fice a ayyukan soja tun bayan shiga rundunar a shekarar 1991. Ya kasance Babban Hafsan Tsaro daga 2023 zuwa watan Oktoban 2025, tare da samun kyaututtuka da dama ciki har da Colin Powell Award for Soldiering a 2012.

An haife shi a Sokoto a 1967, inda ya yi karatunsa na firamare da sakandire, kafin ya tafi Kwalejin Nazari ta Zariya. Daga nan ya shiga Makarantar Horar da Sojoji ta NDA a 1986, inda ya kammala digirinsa a 1991.

Tun daga lokacin, Janar Musa ya rike mukamai da dama a rundunar soja, ciki har da Babban Jami’i mai lura da horo da ayyuka a Hedikwatar Runduna ta 81, Kwamandan Bataliya ta 73, da Mataimakin Darakta a Sashen Tsare-tsaren Runduna.

A 2019 ya jagoranci Sector 3 na Operation Lafiya Dole da kuma Multinational Joint Task Force a yankin Tafkin Chadi. Daga bisani, a 2021, aka nada shi Kwamandan Operation Hadin Kai, sannan ya jagoranci Rundunar Infantry kafin Shugaba Tinubu ya nada shi Babban Hafsan Tsaro a 2023.

A wasikar da ya aika majalisa, Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Janar Musa zai kara karfafawa Ma’aikatar Tsaro gwiwa tare da taimaka wa gwamnati wajen inganta tsaron kasa.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai
Next Post: Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja

Karin Labarai Masu Alaka

Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.