Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya
Published: December 2, 2025 at 2:30 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 2, 2025

Shugaba Tinubu ya mika sunan Janar Christopher Musa domin zama Ministan Tsaron kasar.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya mika sunan tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa, ga majalisar dattawa domin tabbatar da shi a matsayin sabon Ministan Tsaro, bayan murabus da Alhaji Mohammed Badaru Abubakar yayi jiya.

A wata wasika da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, shugaba Tinubu ya ce nadin Janar Musa ya biyo bayan ajiye aiki da Badaru ya yi a ranar Litinin saboda matsalolin lafiya.

Janar Musa, mai shekaru 58 da haihuwa a ranar 25 ga Disamba, ya kasance ɗaya daga cikin manyan hafsoshin soja da suka yi fice a ayyukan soja tun bayan shiga rundunar a shekarar 1991. Ya kasance Babban Hafsan Tsaro daga 2023 zuwa watan Oktoban 2025, tare da samun kyaututtuka da dama ciki har da Colin Powell Award for Soldiering a 2012.

An haife shi a Sokoto a 1967, inda ya yi karatunsa na firamare da sakandire, kafin ya tafi Kwalejin Nazari ta Zariya. Daga nan ya shiga Makarantar Horar da Sojoji ta NDA a 1986, inda ya kammala digirinsa a 1991.

Tun daga lokacin, Janar Musa ya rike mukamai da dama a rundunar soja, ciki har da Babban Jami’i mai lura da horo da ayyuka a Hedikwatar Runduna ta 81, Kwamandan Bataliya ta 73, da Mataimakin Darakta a Sashen Tsare-tsaren Runduna.

A 2019 ya jagoranci Sector 3 na Operation Lafiya Dole da kuma Multinational Joint Task Force a yankin Tafkin Chadi. Daga bisani, a 2021, aka nada shi Kwamandan Operation Hadin Kai, sannan ya jagoranci Rundunar Infantry kafin Shugaba Tinubu ya nada shi Babban Hafsan Tsaro a 2023.

A wasikar da ya aika majalisa, Shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa Janar Musa zai kara karfafawa Ma’aikatar Tsaro gwiwa tare da taimaka wa gwamnati wajen inganta tsaron kasa.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Iran Ta Tasa Keyar Wani Jirgi Shake Da Mai
Next Post: Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja

Karin Labarai Masu Alaka

Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Ana Kokarin Dawo Da Wutan Lantarki A Cuba Afrika
  • Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.