Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki
Published: February 26, 2026 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Afrika ta kudu da Kenya a ranar Alhamis suke kara bayyana cewa ‘yan kasashen masu yawa ne aka yaudare su shiga yakin Rasha da Ukraine, domin hukumomi a Pretoria sun bada rahoton ‘yan kasar biyu sun mutu a fagen daga, yayinda wata kotu a Nairobi ta tuhumi wani mutum da laifin safarar ‘yan kasar 25 domin suyi yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Afrika ta kudu ta fada cewa ‘yan kasar biyu da suka mutu a fagen yaki basa cikin ‘yan kasar su 17 da aka yaudara suka taya Rasha yaki a Ukraine, wadanda galibin su an ceto su sun koma kasar, kamar yadda wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Alhamis. Ma’aikatar bata fadi lokaci da kuma yanayin da ya kai ga mutuwar mutanen biyu ba.

Hukumomin Rasha sun musanta cewa suna daukar ‘yan kasashen Afirka aikin soja ba bisa ka’ida ba domin yakinta da Ukraine.

“gwamnati tana ci gaba da binciken kungiyoyi da suke da hanu wajen daukar ‘yan kasa zuwa Rasha, da zummar hukunta dukkan wadanda suke da hanu ciki,” kamar yadda doka ta tanada, ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta kudun ta fada.

A Nairobi, kotu ta tuhumi wani dan kasar mai suna Festus Arasa Omwamba, darektan wani kamfanin samarwa mutane ayyyukan yi da laifin safarar mutane zuwa Rasha ta hanyoyin yaudara, kamar yadda ofishin Daraktan gabatar da kararraki na kasar ya fada.

Ma’aikatar shari’ar tace an ceto mutane 22 cikin 25, a wani daki a karamar hukumar Machakos da bashi da nisa da babban birnin kasar cikin watan Nuwamban bara. Uku daga cikin wannan adadi tuni suka sapmi kansu a fagen daga a Ukraine.

Fiye da ‘yan kasashen Afirka dubu daya da dari bakwai ne suke yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi
Next Post: Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
  • Hukumomin Kasar China Suna Goyon Bayan Somaliya Labarai
  • Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.