A ranar Alhamis Amurka da kasashen Yamma sun kai ruwa rana da Rasha da China a kan shirin nukiliyar Iran, yayin da Washington ta nemi Majalisar Dinkin Duniya ta kara tabbatar da yakin da ta kaddamar kan Iran makonni biyu da suka gabata.
A wani taro na mambobi 15 na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, wanda Amurka ke jagoranta a wannan watan, Rasha da China sun yi rashin nasara wajen hana tattaunawa kan kwamitin da aka kafa don sa ido da kuma aiwatar da takunkumin da Majalisar Dinkin Duniya ta kakabawa Iran. Inda suka gaza samun kuri’u masu yawa, sun dai samu kuri’u 11 na Rashin amincewa China da Rasha suka kada kuri’u -2 na kin amincewa.
Da yake jawabi ga majalisar, wakilen Amurka a Majalisar Dinkin Duniya Mike Waltz ya zargi Moscow da Beijing da neman kare Tehran ta hanyar toshe ayyukan da ake kira kwamitin 1737.
Waltz ya ce, “Ya kamata dukkan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya su aiwatar da takunkumin hana shigo da makamai masu linzami kan Iran, da haramta safarar makamai masu linzami, da kuma saka danba a kadarorin hada-hadar kudi.”


