Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Published: December 26, 2025 at 1:33 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

A bisa rokon hukumomin Najeriya, mayakan Amurka sun kai hare-hare ta sama a kan sansanonin da aka ce na ‘yan kungiyar Daesh, ko ISIS ne, a jihar Sakkwato dake yankin arewa maso yammacin kasar cikin daren nan da ya shige.

Rahoton farko game da wannan harin ya fito ne daga bakin shugaba Donald Trump na Amurka wanda ya ce a bisa umurninsa, Amurka ta kai munanan hare-hare ta sama a kan ‘yan ISIS wadanda a cewarsa su na kashe kiristoci a yankin.

Daga bisani, rundunar sojojin Amurka mai kula da nahiyar Afirka, AFRICOM, ta fito da wata sanarwar dake cewa an kai wannan harin ne bisa rokon hukumomin Najeriya, kuma an kashe ‘yan ISIS da dama.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, ta fitar da sanarwa dazun nan tana fadin cewa wannan harin da aka kai ya samo asali ne daga yarjejeniyar hadin kan tsaro da musanyar bayanan leke asiri.

Wata sanarwar da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya bayar cikin daren nan, ta tabbatar da cewa lallai Najeriya ce ta bukaci a kai wannan hari kan sansanonin ‘yan ta’addar a karkashin yarjejeniyar hadin kan tsaron da ta kulla da Amurka da nufin shawo kan matsalolin tsaro da suka addabi yankin arewa maso yammacin Najeriya.

Ma’aikatar ta ce gwamnatin Najeriya zata ci gaba da yin aiki da kawayenta ta hanyoyin diflomasiyya da tsaro domin nakkasa ‘yan ta’adda da ayyukansu na ta’addanci a kasar.

A ranar litinin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ba da labarin ewa tun a cikin watan Nuwamba Amurka ta fara shawagin leken asiri a sassa masu yawa na Najeriya.

Gwamnatin Najeriya ta ce wadannan ‘yan bindiga da kuma ‘yan ta’adda ba su ware addini, suna kai hare-harensu a kan Musulmi da kiruista, kuma ikirarin da Amurka keyi na cewa ana kisan kare dangi ma kirista babu ka mshin gaskiya a cikinsa.

Najeriya ta yarda zata yi aiki da Amurka wajen karfafa yakar wadannan ‘yan ta’adda.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa
Next Post: Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wakilan Rasha Da Ukraine Sun Tattauna A Abu Dhabi Ranar Juma’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojin Saman Najeriya Sunyi Gagarumar Nasara A Yankin Borno Najeriya
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.