Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Damke Matasa Masu Gurza Kudaden Ketare Na Jabu
Published: November 21, 2025 at 11:27 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar sun dakile wani yunkurin baza kudaden Jabu a harakokin hada hadar kudaden kasar.
Dubban takardun Euro da a ka kyasta cewa darajarsu ta haura milion 600 na CFA ne a ka cafke a hannun wasu matasa a birnin Yamai, lamarin da ya sa al’umma ta jinjinawa jami’an tsaro tare da jan hankulan hukumomi su karfafa matakan tsaro.
Bayanan sirrin da rundunar tsaron Garde Nationale ta bibiya ne suka bai wa dakarunta damar gano wani gida da ke anguwar Nord Lazaret ta birnin Yamai inda ake buga takardun kudade na Jabu.
A yayin samamen da suka kai jami’an tsaro sun kama wasu mutane biyu dukkansu matasan masu kimanin shekaru 30, an same su dauke da dubban takardun kudaden Euro dari biyu-biyu, hade da wasu sinadaran da aka ayyana a matsayin na wankin takardar kudi.
Da ta ke  bayyana ra’ayinta kan wannan al’amari Mme Adji Gana Fatouma Souleymane na cewa.
“An kyasta cewa darajar wadanan takardun kudaden Euro na Jabu sun haura milion 600 na CFA wadanda idan aka yi nasarar shigar da su, babbar barzana ce ga tattalin arziki” inji sakataren watsa labaran kungiyar FRSA Salissou Ibrahim.
Buga kudin Jabu na daga jerin miyagun aiyukan da a ka gano cewa suna kokarin samun gindin zama a Nijar, abin da wani mazaunin Yamai Laouali Boubacar yace ya kamata hukumomi su taka musu burki tun da wuri.
Mutanen da rundunar tsaron ta Garde Nationale ta kama ko ba ya ga takardun kudaden Jabu an same su da kakin Soja da tufafin wasannin motsa jiki masu dauke da tambarin ‘yan Sanda.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Manuniya Kashi Na Daya, Yau Juma’a 11.21.25
Next Post: Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini Afrika
Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.