Hukumomin tsaron kasar Libya sun kubutar da bakin haure fiye da 200 daga wani kurkukun sirri da aka gina a karkashin kasa a garin Kufra dake yankin kudu maso gabashin kasar, a inda aka tsare su cikin wani mummunan yanayi.
Wasu majiyoyin tsaro biyu a kasar sun ce hukumomi sun gano wannan kurkuku da aka gina mai zurfin mita 3 a karkashin kasa a garin na Kufra wanda wani madugun ‘yan safarar mutane na Libya yake gudanar da shi.
Daya daga cikin majiyoyin yace har yanzu ba a kama mutumin da ya gina yake gudanar da wannan kurkuku na sirri ba.
Majiyar ta ce wasu daga cikin wadannan bakin haure sun shafe shekaru 2 suna daure a ciki. Daya majiyar kuma ta ce sumamen da aka kai ya bankado laifi na cin zarafin bil adama mafi muni da aka taba ganowa a yankin.
Bakin hauren da aka kubutar daga wannan bala’i sun fito ne daga kasashen kudu da hamadar Sahara, kuma akasarinsu daga kasashen Somaliya da Eritrea, kuma sun hada da mata da yara kanana. Garin Kufra yana gabashin Libya, kimanin kilomita 1700 daga Tripoli, babban birnin kasar.
Tun bayan da kungiyar kawancen tsaro ta NATO ta taimaka wa ‘yan tawaye wajen kawarwa da kashe shugaba Muammar Gaddafi a 2011, Libya ta zamo zangon safarar bakin hauren dake tserewa daga yake-yake da talauci, wadanda ke bi ta wannan hanya mai hatsarin gaske ta cikin hamada bisa zummar samun hanyar kaiwa kasashen Turai.
A makon da ya shige ma, an gano gawarwakin bakin haure su 21 a wani ramin da aka haka aka binne su a yankin na gabashin Libya, inda aka samu wasu da suka kubuta da rayukansu da aka ga alamun an gana musu azaba kafin a sake su


