Masu gabatar da kara sun gabatar da takarda gaban kotu yau, inda suke zargin mutane 9 da alhakin kai hari a kauyen Yelwa dake jihar Benue a Nigeria, a watan Yunin bara, da yayi sanadiyyar rayuka 150.
A karar da aka gabatar gaban babbar kotu a Abuja, An yi zargin wadanda ake tuhuma da cewa sun shirya abun ne, sun samo makamai, suka kuma samo mutane daga jihohi da dama don aiwatar da manufar tasu.
Masu gabatar da kara sun ce babban su Ardo Lawal Muhammad tare da wasu sun gana a jihar Nassarawa don sun harhada kudi, su bayar da umarnin yadda za’a kai harin, kuma su samo mutane da zasu taya su. Wasu da daman su ana tuhumar su da samar da bindigogi kirar AK47, taimakawa ‘yan bindiga, da kuma samun kebantaccen wuri don yin shirin aiwatar da mugun nufin su.
Harin da aka kai yayi sanadiyar konewar gidaje, tare da salwantar da rayukun mutane da dama a kauyen Yelwata dake gundumar Guma a jihar Benue.


