Asusun bada lamuni na duniya wato IMF a takaice, zai kai ziyarar aiki kasar Gabon cikin watan gobe, a wani bangare na aiki da hukumomin kasar, duk da cewa babu zancen karbar rance da aka yi tsakanin kasar da asusun a hukumance, kamar yadda wani kakakin asusun bada lamunin ya fada ranar jumma’a.
Gabon tana kara dogaro kan samun rance daga hukumomi masu hada-hadar kudi dake yankin, koda shike kamfanin auna karfin tattalin arziki na kasashe da ake kira Fitch, tace kasar ta rage karbar bashi, bayan da kamfanin ya rage karfin wasu masu baiwa kasar rance daga ketare.
Thierry Minko, wanda a farkon shekaran nan aka nada ministan kudi da tattalin arziki na kasar Gabon, ya fada a farkon makon nan cewa, kasar zata aiwatar da shirin habaka tattalin arziki, tare da taimakon asusun bada lamunin, kuma aka karfafa shawarwari da asusun bada lamunin.
Wani kakakin asusun bada lamunin wato IMF a takaice yace sabuwar gwamnatin kasar a Gabon ta karfafa shawarwari da asusun tun bayan da kasar ta aiwatar da wani garambul.


